| Hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
An kama mutanen da suka jagoranci harin Sierra Leone — Shugaba Bio
Shugaban Saliyo Julius Maada Bio ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin da ya faru tare da tabbatar da cewa za a hukunta wadanda suka yi kokarin hargitsa kasar.
An kama mutanen da suka jagoranci harin Sierra Leone — Shugaba Bio
Maharan sun kai hari cikin barikin sojoji da kuma gidan yari. / Hoto: Reuters / Others

Shugaban Saliyo Julius Maada Bio ya bayyana cewa jami’an tsaro sun kama “akasarin shugabannin” wadanda suka yi kokarin hargitsa kasar.

Ya bayyana haka ne a jawabin da ya yi wa 'yan kasar ta gidan talbijin ranar Lahadi da maraice.

“An kama akasarin shugabanninsu. Ana ci gaba da gudanar da bincike,” kamar yadda shugaban kasar ya bayyana.

Wannan na zuwa ne bayan harin da wasu ‘yan bindiga suka kai barikin sojoji inda suka fasa wurin da ake ajiye makamai. Haka kuma maharan sun fasa gidan yarin kasar inda suka saki fursunoni.

Hadin kan kasa

Shugaba Bio ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta tabbatar an hukunta wadanda aka kama da laifi bayan an bi ka’ida.

Ya kuma yi kira ga ‘yan kasa su hada kansu inda ya ce “karfinmu ya dogara ne kan hadin kanmu” inda kuma ya tabbatar wa ‘yan kasar cewa gwamnatinsa za ta samar da zaman lafiya da tsaro a cikin kasar.

Kungiyar ECOWAS ta nuna rashin jin dadinta kan lamarin da ya faru a Saliyo a ranar Lahadi.

“Kungiyar ECOWAS ta ji labarin wannan abin kyamar da wasu mutane suka dauki makamai da niyyar kawo cikas ga zaman lafiya da kuma dokar da kundin tsarin mulki ya tanada a Saliyo,” kamar yadda kungiyar ta bayyana a wata sanarwa.

“ECOWAS ta yi Allah wadai da wannan lamarin inda take kira kan a kama tare da hukunta wadanda suke da hannu a lamari. ECOWAS na kara jaddada cewa ba za ta lamunci sauyin gwamnati ba bisa ka’idar kundin tsarin mulki ba.”

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Ɗalibai 16 sun rasu sakamakon gobara a wata makarantar 'yanmata a Kenya
Ghana ta kwashe 'yan ƙasarta 300 daga Afirka ta kudu yayin da ake zanga-zanga kan baƙin haure
Mutane uku sun mutu bayan motar fasinja ta yi karo da giwa a gandun dajin Uganda
Shugaban Senegal Faye ya naɗa sabon firaminista da zai maye gurbin Sonko
Adadin mutanen da Ebola ta kashe a Jamuhuriyar Kongo ya wuce 200
Shugaban Senegal Faye ya sallami Firaministansa Ousmane Sonko
Kenya za ta rage farashin man dizel bayan zanga-zangar da aka yi kan tsadar makamashi
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar za ta ƙayyade kuɗin gidajen haya
Sierra Leone ta amince ta karɓi kashin farko na waɗanda aka taso ƙeyarsu daga Amurka
'Makashin Al Fasher' ya koma fagen daga a yaƙin Sudan: Rahoto
Nijar da China sun cim ma yarjejeniyar mai bayan watanni ana takaddama
Adadin mutanen da suka mutu a Congo saboda kamuwa da Ebola ya kai 131
Kenya ta kama wata mata bisa zargin damfarar Ba’amurke dala 431,000 a yarjejeniyar cinikin zinare
Dole Afirka ta daina bin umarnin manyan ƙasashen duniya
WHO ta bayyana ɓarkewar Ebola a Jamhuriyar Kongo a matsayin 'matsalar lafiya ta gaggawa'
Mutum 80 sun rasu a sabuwar ɓarkewar Ebola a Jamhuriyar Congo
Sojojin Sudan sun ƙwace iko da wani muhimmin birni a kusa da iyakar Habasha bayan arangama da RSF
Yakin Sudan: Yara na daga gomman da aka kashe a arangamar makonni biyu a Kordofan
Nijar na son ƙara adadin jihohinta daga 8 zuwa 19 da kuma sauya sunayen wasu jihohim
Shirin 'Big Catch-Up': Kokarin da ya kawo alluran rigakafi miliyan 100 ga yaran Afirka da aka manta