| Hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
An kama mutanen da suka jagoranci harin Sierra Leone — Shugaba Bio
Shugaban Saliyo Julius Maada Bio ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin da ya faru tare da tabbatar da cewa za a hukunta wadanda suka yi kokarin hargitsa kasar.
An kama mutanen da suka jagoranci harin Sierra Leone — Shugaba Bio
Maharan sun kai hari cikin barikin sojoji da kuma gidan yari. / Hoto: Reuters / Others
27 Nuwamba 2023

Shugaban Saliyo Julius Maada Bio ya bayyana cewa jami’an tsaro sun kama “akasarin shugabannin” wadanda suka yi kokarin hargitsa kasar.

Ya bayyana haka ne a jawabin da ya yi wa 'yan kasar ta gidan talbijin ranar Lahadi da maraice.

“An kama akasarin shugabanninsu. Ana ci gaba da gudanar da bincike,” kamar yadda shugaban kasar ya bayyana.

Wannan na zuwa ne bayan harin da wasu ‘yan bindiga suka kai barikin sojoji inda suka fasa wurin da ake ajiye makamai. Haka kuma maharan sun fasa gidan yarin kasar inda suka saki fursunoni.

Hadin kan kasa

Shugaba Bio ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta tabbatar an hukunta wadanda aka kama da laifi bayan an bi ka’ida.

Ya kuma yi kira ga ‘yan kasa su hada kansu inda ya ce “karfinmu ya dogara ne kan hadin kanmu” inda kuma ya tabbatar wa ‘yan kasar cewa gwamnatinsa za ta samar da zaman lafiya da tsaro a cikin kasar.

Kungiyar ECOWAS ta nuna rashin jin dadinta kan lamarin da ya faru a Saliyo a ranar Lahadi.

“Kungiyar ECOWAS ta ji labarin wannan abin kyamar da wasu mutane suka dauki makamai da niyyar kawo cikas ga zaman lafiya da kuma dokar da kundin tsarin mulki ya tanada a Saliyo,” kamar yadda kungiyar ta bayyana a wata sanarwa.

“ECOWAS ta yi Allah wadai da wannan lamarin inda take kira kan a kama tare da hukunta wadanda suke da hannu a lamari. ECOWAS na kara jaddada cewa ba za ta lamunci sauyin gwamnati ba bisa ka’idar kundin tsarin mulki ba.”

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina
Sudan ta yi Allah wadai da 'mummunan' harin da RSF ta kai wani asibiti yayin allurar rigakafin yara
Ghana za ta fara aiwatar da shirin shiga ƙasar ba tare da biza ba ga dukkan 'yan Afirka
Shugaban riƙon jihar Kudu maso yammacin Somaliya zai hau kan mulki bayan ajiye aikin shugaba
Sudan ta nemi 'yan ƙasar da suka yi ƙaura zuwa ƙasashen waje saboda yaƙi su koma gida
Hukumar leƙen asirin Somalia ta kashe masu haɗa bama-baman Al Shabab
Mali ta musanta rahoton sakin ’yanta’adda 200 domin samun man fetur
An kasa cim ma matsaya kan sabbin sauye-sauye a tattaunawar WTO a Kamaru
Darasin da Togo ke koya wa sauran kasashe wajen magance cututtukan da aka yi watsi da su
’Yanbindiga sun kashe fararen-hula 16 kusa da iyakar Nijar da Mali
Nijar ta ƙaddamar da sabon katin ɗan ƙasa na zamani mai tambarin AES
Laifi mafi muni: AU ta nemi MƊD ta ɗauki mataki kan biyan diyyar cinikin bayi bayan MƊD ta tabbatar
Ghana ta sake yin bita kan tsarin yaƙi da ta’addanci sakamakon barazanar masu tsattsauran ra’ayi
Rasha ta yi iƙirarin cewa 'yan kwangilar sojin Faransa na da yawa a Afirka
Hukumomi a Nijar sun kama wani mutum a Zinder bisa zargin yawan kai wa 'mata' hari a kan babur
Me ya sa diyyar cinikin bayi da mulkin mallaka suka zama masu muhimmanci ga Afirka a 2026
Hatsarin jirgin ruwa ya yi ajalin mutane tara, wasu da dama sun ɓata a gaɓar tekun Djibouti
MDD ta ayyana cinikin bayi a Afirka a matsayin ‘laifi mafi muni ga ɗan'adam'
Shugaban Ghana ya faɗa a New York cewa Amurka tana goge tarihin baƙar-fata