| Hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
An kashe 'yan bindigar Zamfara 100 bayan an yi musu 'luguden wuta'
Yayin kai musu farmakin, an samu hadin gwiwa tsakanin dakarun sojin sama da na kasa, kamar yadda rahotanni suka bayyana.
An kashe 'yan bindigar Zamfara 100 bayan an yi musu 'luguden wuta'
Nijeriya na amfani da jiragen yaki wajen fatattakan barayin daji:Hoto/Facebook/Nigeria Air Force HQ / Others

Kasa da kwana daya bayan Hafsan Hafsoshin Sojin Nijeriya Janar Christopher Musa ya bukaci dakatun kasar da su fatattaki 'yan bindiga, an kashe 'yan bindiga fiye da 100 bayan wani hari da aka kai ta sama a yankin Arewa-maso Yammacin Nijeriya.

Kafar yada labarai ta PR Nigeria ta ruwaito cewa an yi wani aikin hadin gwiwa na soji bayan da aka samu sahihan bayanan sirri a wasu wurare da 'yan bidigar suke buya a yankunan jihohin Kebbi da Zamfara.

Yayin kai musu farmakin, an samu hadin gwiwa tsakanin dakarun sojin sama da na kasa, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

“Kwamandan Rundunar Hadarin Daji ya ce sun yi nasarar kawar da 'yan ta'adda da dama da shugabanninsu a yankin Sangeko da Karamar Hukumar Maru a jihar Zamfara.

"An gano 'yan bindigar ne bayan samun wasu bayanan sirri daga wurare daban-daban da kuma shirinsun na nausawa yankunan jihar Neja. 'Yan ta'addan suna tafiya a ayarin babura da yawa a hanyar garin Kabaro zuwa Sangeko.

"Bayan haka an kai wa 'yan ta'addan hari ta sama inda aka kawar da dama daga cikinsu. Haka zalika an lalata babura".

Mai magana da yawun Rundunar Sojin Saman Nijeriya Air Commodore Edward Gabkwet ya tabbatar da faruwar al'amarin ga kafar yada labarai ta PR Nigeria. Sai dai bai yi karin haske ba kan adadin mutanen da suka mutu ko jikkata ba sanadin farmakin.

"Farmakin da aka kai a yankin ya samu nasara sosai, sai dai ba zan iya cewa komai ba dangane da alkaluma saboda farmaki ne da ake ci gaba da yi," in ji shi.

A ranar Talata yayin da ya kai ziyara Maiduguri, Hafsan Hafsoshin Sojin Nijeriya Janar Christopher Musa ya bukaci dakarun kasar da kada su rika jira sai 'yan Boko Haram sun kai musu hari kafin su tunkare su.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Fiye da mutum 7,000 sun kamu da annobar Ebola a Jamhuriyar Kongo
Shugaban Nijar ya naɗa Birgediya Janar Mamane Sani Kiaou a matsayin sabon shugaban hafsan sojoji
FIFA ta musanta iƙirarin Maroko na 'karɓar baƙuncin' wasan ƙarshe na Gasar Kofin Duniya na 2030
Majalisar Sudan ta cire 'yantawayen RSF daga tattaunawar ƙasa
An raba mutane fiye da 4,500 da gidajensu a Darfur ta Kudu da Blue Nile saboda matsalar tsaro
An ceto fiye da 'yan ci-rani 1,000 kusa da tekun yammacin Afirka cikin mako ɗaya, in ji MSF
Shugaban Zambia Hichilema ya yi farin ciki da masoyan da suka ba shi kyautar kazar gida
Gwamnatin Ghana ta kashe $4.37m don kwashe 'yan ƙasarta daga Afirka ta Kudu
Gwamnatin Nijar ta yi kira ga jama'a su duƙufa da Al-Ƙunut domin neman tsari daga 'maƙiyan ƙasa'
Kwalara ta kashe mutum 23 a Sudan, fiye da 310 sun kamu da cutar
Majalisar Dinkin Duniya ta amince a sake zana taswirar Afirka zuwa ainihin yadda nahiyar take
Nijar na zargin Faransa da tunzura sojojin da suka yi yunkurin tawayen da aka dakile
Tallafin ƙasashen waje da harin jiragen sama marasa matuƙa sun ƙara tsananta yaƙin Sudan - MDD
Babban hafsan sojin Sudan Burhan na rangaɗi game da shirin yaƙi a fagen yaƙin Blue Nile
Dubban mutane sun yi zanga-zanga don nuna goyon bayansu ga sojin Nijar bayan dakile yunƙurin tawaye
Hatsarin mota a Masar ya yi ajalin mutum 16 a sanannen yanki mai cike da ‘yan yawon bude ido
Shugaban ƙungiyar Tarayyar Afirka ya yi Allah wadai da boren da aka yi a Nijar
An kama ‘yar jarida mai yawan mabiya Denise Dusauchoy ‘yar kasar Kongo a Tanzania
Tebboune ya sake bayyana goyon bayan Aljeriya ga Nijar yayin da ake fuskantar barazanar tsaro
Yadda maganin rana guda zai iya kawo ƙarshen cutar bacci a Afirka