| Hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
Lucky Aiyedatiwa na APC ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Ondo
Aiyedatiwa ya samu ƙuri’u 366,781 a zaɓen jihar inda ya kayar da babban abokin adawarsa Ajayi Agboola na Jam’iyyar PDP wanda ya samu ƙuri’u 117,845, kamar yadda hukumar ta INEC ta sanar.
Lucky Aiyedatiwa na APC ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Ondo
'Yan takara 18 ne suka fafata a zaɓen na Jihar Ondo wanda aka gudanar a ranar Asabar. / Hoto: Luck Aiyedatiwa / Others

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta ayyana Lucky Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Ondo.

Hakan na nufin Aiyedatiwa zai ci gaba da zama a gidan gwamnatin jihar Ondo har zuwa lokacin da za a rantsar da shi a matsayin sabon gwamnan jihar a karo na biyu bayan ya gaji Rotimi Akeredolu wanda ya rasu a watannin baya.

Aiyedatiwa ya samu ƙuri’u 366,781 a zaɓen jihar inda ya kayar da babban abokin adawarsa Ajayi Agboola na Jam’iyyar PDP wanda ya samu ƙuri’u 117,845, kamar yadda hukumar ta INEC ta sanar.

An samu tazarar ƙuri’u 248,936 tsakanin ‘yan takarar wanda hakan ke nufin Aiyedatiwa ya ninka abokin takararsa a yawan ƙuri’u.

Haka kuma sakamakon zaɓen ya nuna jam’iyyar ta APC ta samu nasara a duka ƙananan hukumomi 18 na jihar Ondo.

'Yan takara 18 ne suka fafata a zaɓen na Jihar Ondo wanda aka gudanar a ranar Asabar.

An tsaurara tsaro a jihar a yayin zaɓen inda aka jibge sama da 'yan sanda 22,000 a jihar.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Harin kare kan wata 'yar Afirka ta Kudu ya janyo kiraye-kirayen dokoki masu tsauri
Kotun Sudan ta yanke wa shugaban RSF Hemedti hukuncin kisa kan kashe tsohon gwamnan Darfur ta Yamma
Gwamnatin Mali ta tabbatar da kashe sojoji 30 a wani harin ta'addanci a arewacin ƙasar
Aikin matatar man Dangote zai ci gaba a gaɓar tekun  Kenya, a cewar Shugaba Ruto
Afirka ta sami tallafin $900m domin faɗaɗa fasahar girki na zamani mara gurɓata muhalli
Rasha na son ƙarfafa alaƙa da Ƙawancen Ƙasashen Sahel (AES) - Lavrov
Sojojin Sudan sun ƙwace ƙauyen Al-Kurmuk bayan arangama da dakarun RSF
Jami'an tsaro a Afirka ta Kudu sun kama masu haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba fiye da 200
Ƙawancen tsaro na Turkiyya da Afirka na haɓaka a tsarin duniya da ke sauyawa
Jami’an leken asiri sun lalata yunƙurin ‘yan ta’addan Daesh na kai hari a garuruwan Morroco bakwai
'Yansandan Afirka Ta Kudu sun ce mutuwar ɗan Nijeriya ba ta da alaƙa da tashin hankalin ci-rani
MDD ta yi gargaɗin cewa hare-haren RSF na iya mayar da birnin Al-Obeid na Sudan kamar Al-Fasher
Rikicin diflomasiyya ya kaure tsakanin Ghana da Afirka ta Kudu kan mutuwar ɗan Ghana
Burkina Faso, Mali da Nijar sun gabatar da sanarwar ficewa daga ICC, in ji kotun
Sojojin Mali sun raka motocin dakon mai da abinci 940 zuwa Bamako saboda fargabar harin ta'addanci
Sojojin Burkina Faso sun ce sun kashe 'yanta'adda fiye da 400 a wani hari da suka daƙile
An gurfanar da ɗalibai mata takwas a kotu a Kenya kan zargin kisan abokan karatunsu a gobara
Yadda Nijeriya ke fama da hauhawar farashin gas din girki
MDD ta yi gargaɗin cewa cutar Ebola na iya jefa kusan mutane miliyan 1 cikin talauci a DRC
Afirka ta Kudu ta mai da fiye da mutum 25000 kasashensu kafin wa'adin 30 ga Yuni na masu ƙyamar baƙi