| Hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Ana zaben jin ra'ayin jama'a kan wa'adin shugaban kasa a Jamhuriyar Tsakiyar Afirka
A zaben jin ra'ayin jama'a kan gyara kundin tsarin mulki, mutanen Jamhuriyar Tsakiyar Afirka suna kada kuri'a kan canja wa'adin mulkin shugaban kasa ko kuma a bar shi a yadda yake.
Ana zaben jin ra'ayin jama'a kan wa'adin shugaban kasa a Jamhuriyar Tsakiyar Afirka
Faustin-Archange Touadera ne ke shugabancin Jamhuriyar Tsakiyar Afirka tun watan Maris din shekarar 2016. / Others
30 Yuli 2023

Ana zaben jin ra'ayin jama'a a Jamhuriyar Tsakiyar Afirka kan yiwuwar gyara kundin tsarin mulki a ranar Lahadi, wanda idan aka amince, za a daina kayyade wa'adin mulkin shugaban kasa,

Hakan zai bai wa Shugaba Faustin-Archange Touadera damar sake tsayawa takara a karo na uku a shekarar 2025.

An fara zabar Touadera ne a shekarar 2016 a wa'adin shekara biyar kuma ya sake yin nasara a zabe a shekarar 2020 wanda ya kamata ya zama wa'adinsa na karshe a kan karagar mulki.

Sabon tsarin mulkin zai ba shi damar sake neman sabon wa'adin shekara bakwai, kuma daga nan ne babu wani sauran kayyade wa'adin mulki ga shi ko kuma wani da zai yi takarar kujerar shugaban kasa.

Jam'iyyun 'yan hamayya da wasu kungiyoyin fararen-hula sun yi kira da a kauracewa zaben, inda suka ce da ma an kitsa Shugaba Touadera ya ci gaba da zama a kan kujerar mulki har tsawon rayuwarsa.

An samu karancin fitowar masu kada kuri'a, inda a wata rumfar zabe a arewacin wajen birnin Bangui da safiyar ranar Lahadi aka samu masu kada kuri'a kamar dozin biyu a kan layi, kamar yadda wani wakilin kamfanin dillancin labarai na Reuters ya bayyana.

"Ina fatan abokaina za su fito da yawansu su kada kuri'a. Abin da nake so shi ne kasar nan ta samu kwanciyar hankali da ci gaba," in ji Laurent Ngombe, wani malamin makaranta wanda yake cikin mutanen da suka fara kada kuri'arsu.

Kasar wadda ba ta da teku, wadda kuma girmanta ya kai na kasar Faransa da ke da yawan jama'ar da ya kai miliyan 5.5, tana da albarkatun kasa kamar zinare da lu'u- lu'u da kuma timba.

Ta fada halin rashin tabbas iri-iri, ciki har da juyin mulki a karo da dama da bore, tun bayan da ta samu 'yancin kai daga Faransa a shekarar 1960.

Touadera, mai shekara 66, wanda masanin fannin lissafi ne, ya yi kokarin dakile boren da wasu kungiyoyi suke masa a kasar tun bayan kifar da tsohon Shugaba Francois Bozize sanadin wani bore da aka yi masa a shekarar 2013.

Shugaba Touadera ya nemi taimakon Rasha wajen dakile boren da ake masa a shekarar 2018.

Tun daga lokacin ne kusan dakaru 1,500 ciki har da sojojin haya na kungiyar Wagner ta Rasha, aka aika kasar tare da sojojin kasar.

MAJIYA:Reuters
Rumbun Labarai
Nijar ta ƙaddamar da sabon katin ɗan ƙasa na zamani mai tambarin AES
Laifi mafi muni: AU ta nemi MƊD ta ɗauki mataki kan biyan diyyar cinikin bayi bayan MƊD ta tabbatar
Ghana ta sake yin bita kan tsarin yaƙi da ta’addanci sakamakon barazanar masu tsattsauran ra’ayi
Rasha ta yi iƙirarin cewa 'yan kwangilar sojin Faransa na da yawa a Afirka
Hukumomi a Nijar sun kama wani mutum a Zinder bisa zargin yawan kai wa 'mata' hari a kan babur
Me ya sa diyyar cinikin bayi da mulkin mallaka suka zama masu muhimmanci ga Afirka a 2026
Hatsarin jirgin ruwa ya yi ajalin mutane tara, wasu da dama sun ɓata a gaɓar tekun Djibouti
MDD ta ayyana cinikin bayi a Afirka a matsayin ‘laifi mafi muni ga ɗan'adam'
Shugaban Ghana ya faɗa a New York cewa Amurka tana goge tarihin baƙar-fata
Iskar kasar Chadi ce mafi muni da rashin inganci a Afirka a 2025 - Rahoto
Ranar Tarin Fuka ta Duniya: Yadda injinan GeneXpert suke sauya yaƙi da cutar TB a Togo da Congo
Ghana ta buƙaci taimakon MDD don warware batun cinikin bayi saboda ƙarfafa ƙoƙarin neman biyan diyya
Makomarmu ba ta sayarwa ba ce: Abin da ya sa dole matasan Afirka su nemi ba’asin haraji da cin bashi
Me ya sa yawancin tutocin kasashen Afirka suke da kamanceceniyar kaloli?
Aƙalla mutum 81 sun mutu cikin makonni sakamakon ambaliyar ruwa a Kenya
An kashe mutum 64, cikinsu har da ƙananan yara 13, a harin asibitin Sudan — WHO
Eid al-Fitr: Hotunan yadda aka yi bikin ƙaramar Sallah a ƙasashen Afirka
Nijeriya ta zama ta huɗu yayin da Sahel ke kan gaba a yawan kashe-kashe na ta'addanci —Rahoto
Yadda duniya ta rungumi shan gahawa kuma manoma a Afirka suke samun alheri
An kawar da mazan jiyan Kamaru yayin da majalisar dokokin ta zaɓi sabbin shugabanni