Daga trtafrikahau
Hukumar Tsaron Kasa ta Jamhuriyar Nijar ta ce sojojin kasar bakwai ne suka rasa rayukansu sakamakon taka nakiyar da aka binne a hanya ranar Lahadi, a yankin Tillaberi.
Wata sanarwa da hukumar ta fitar ta ce lamarin ya rutsa da motar soji mai safarar kaya mako-mako a yankin da ke da nisan kilomita shida daga kauyen Samira.
Kamfanin dillancin labarai na AFP ya rawaito cewa wasu sojojin sun jikkata.
ZA KU SO WAƊANNAN
Mayakan da ke ikirarin jihadi suna yawan kai hare-hare a yankin da ke kan iyaka da Burkina Faso.
Sojojin Nijar suna fuskanta hare-hare daga ‘yan ta’adda da suka hada da Boko Haram, da al-Qa’ida, da Islamic State.
Hare-haren na ci gaba duk da cewa manyan kasashe masu karfin soji, wato Faransa da Amurka suna tallafa wa kasar da kayan aiki.
MAJIYA:AFP















