| Hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Nijeriya ta bukaci sojojin Nijar su bar Bazoum 'ya koma wata kasa'
Shugabannin ECOWAS za su yi taro a Abuja babban birnin Nijeriya a ranar 10 ga watan Disamba domin tattaunawa kan halin da yankin yake ciki.
Nijeriya ta bukaci sojojin Nijar su bar Bazoum 'ya koma wata kasa'
An yi wa Bazoum juyin mulki tun a watan Yulin 2023 kuma tun a lokacin yake a tsare. / Hoto: AFP / Others

Nijeriya na kara jaddada kira kan a saki tsohon shugaban Nijar da aka hambarar Mohamed Bazoum, tare da rokon sojojin da ke mulkin kasar kan su bar shi ya tafi kasar da yake so.

Nijeriya ce a halin yanzu ke jagorantar kungiyar ECOWAS wadda ta saka wa Nijar din takunkumi tun bayan da sojoji suka yi juyin mulki a watan Yuli.

ECOWAS ta jima tana son a saki Bazoum nan take domin komawa kan kujerar shugabanci, sai dai sojojin da ke mulkin kasar na ci gaba da tsare shi inda sojojin suka ce za a iya shafe shekara uku kafin a koma kan mulkin dimokuradiyya a kasar.

“Muna son a saki Shugaba Bazoum ta yadda zai iya barin Nijar,” kamar yadda Ministan Harkokin Wajen Nijeriya Yusuf Tuggar ya shaida wa kafar watsa labarai ta Channels a Nijeriya.

‘Cire takunkumi ‘

“Ba zai ci gaba da zama a tsare ba. Zai tafi wata kasa wadda aka amince. Daga nan ne za mu fara magana kan batun cire takunkumi.” Ya bayyana cewa har yanzu ECOWAS a shirye take domin tattaunawa da sojojin Nijar.

“Kun san cewa damar na nan. A shirye muke a ko da yaushe, za mu iya sauraren su, wuka da nama na hannunsu.”

Shugabannin ECOWAS za su yi taro a Abuja babban birnin Nijeriya a ranar 10 ga watan Disamba domin tattaunawa kan batun yankin, wanda ya kasance yana fusknatar juyin mulkin soji tun daga shekarun 2020, kama daga Mali zuwa Burkina Faso da Guinea da Nijar.

‘Yunkurin juyin mulki’ a Saliyo da Guinea-Bissau

A watan da ya gabata, wani yunkurin juyin mulki a Saliyo ya yi sanadin mutuwar mutum 21, kamar yadda manyan jami’an gwamnatin kasar suka tabbatar a kasar wadda ke cikin kasashen ECOWAS.

Ita ma Guinea-Bissau wadda kasa ce ta ECOWAS, shugabanta Umaro Sissoco Embalo a ranar Asabar ya ce rikicin da aka yi a wannan makon wanda a ciki akwai wasu daga cikin dogaran kasar “yunkuri ne na juyin mulki.”

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Babban hafsan sojin Sudan Burhan na rangaɗi game da shirin yaƙi a fagen yaƙin Blue Nile
Dubban mutane sun yi zanga-zanga don nuna goyon bayansu ga sojin Nijar bayan dakile yunƙurin tawaye
Hatsarin mota a Masar ya yi ajalin mutum 16 a sanannen yanki mai cike da ‘yan yawon bude ido
Shugaban ƙungiyar Tarayyar Afirka ya yi Allah wadai da boren da aka yi a Nijar
An kama ‘yar jarida mai yawan mabiya Denise Dusauchoy ‘yar kasar Kongo a Tanzania
Tebboune ya sake bayyana goyon bayan Aljeriya ga Nijar yayin da ake fuskantar barazanar tsaro
Yadda maganin rana guda zai iya kawo ƙarshen cutar bacci a Afirka
Mayaƙa 200 sun fice daga RSF ta Sudan inda suka sauya sheƙa zuwa rundunar sojin ƙasar
Ghana ta kama mabarata fiye 1,000 a Accra da Kumasi – Hukumar Shige ta Fice ta Ghana
Algeria ta aika jiragen yaƙi huɗu zuwa Jamhuriyar Niger bayan tashin hankali a Niamey
Sojin ruwan Turkiyya da dakarun Somaliya sun ceto jirgin dakon kaya daga 'yanfashin teku
Boren soji a Yamai: AES ta jaddada goyon bayanta ga Nijar, ta yaba wa martanin dakarun tsaro
’Yan a-waren azbinawa sun saki sojojin Mali 60 da suka sace
An ji karar harbe-harben bindiga a kusa da sansanin soji da kuma fadar shugaban kasa a Nijar
Traore ya buƙaci matasan Burkina da su guji bin 'ɓarauniyar hanya' wadda ke kaiwa ga cin amana
Sojojin Sudan sun yi ikirarin harbo wani jirgi maras matuƙi kusa da iyakar Habasha
Gwamnatin Ghana ta yi watsi da gudunmawar cedi miliyan 20 daga kamfanin MTN
Manufar Afirka ta shiga ofis mafi girma a MDD: Ko hakan ba zai iya sake faruwa ba?
Nijar ta cim ma yarjejeniyar gina tashar samar da wutar lantarki ta hasken rana mai karfin MW 200
Gwamnatin Ghana za ta kawo ƙarshen binciken da ‘yansanda ke yi na ababen hawa a kan hanya