| Hausa
TURKIYYA
3 MINTI KARATU
Turkiyya na samar da mafita a bangarorin da MDD ta nuna gazawa: Fahrettin Altun
Jamhuriyar Turkiyya ta zama kasar da ke kan gaba a yankin da take a daidai lokacin da ta shiga karni na biyu, in ji Daraktan Watsa Labarai na Turkiyya Fahrettin Altun.
Turkiyya na samar da mafita a bangarorin da MDD ta nuna gazawa: Fahrettin Altun
Domin shawo kan matsalolin duniya da na yankuna, Turkiyya na amfani da hanyoyin jinkai da na diflomasiyya, in ji Fahrettin Altun. /Hoto:AA / AA

Manyan kungiyoyin duniya irin su Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya sun gaza wurin shawo kan matsalolin duniya inda suka kara "ta'azzara" su, in ji Daraktan Watsa Labarai na Turkiyya.

A wata makala da ya rubuta a wata mujalla ta Sifaniya mai suna Atalayar a ranar Asabar, Fahrettim Altun ya bayyana cewa "a bayyane take cewa dole ne a kafa kungiyoyin kasa da kasa bisa la'akari da sabon karni da sabon zamani, tare da la'akari da yadda sabbin abubuwa ke daidaita."

A makalar mai taken "Turkiyyar Erdogan na samar da mafita a wuraren da Majalisar Dinkin Duniya ta gaza", Altun ya ce Ankara na shirin amfani da hanyoyi daban-daban wadanda suka zo daidai da tsarin Shugaba Recep Tayyip Erdogan yake yawan magana a kai na cewa, "Duniya ta fi biyar girma," inda yake nufin mambobin dindindin na Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya wadanda suka hada da Amurka da Birtaniya da Faransa da Rasha da China.

Domin magance matsalolin duniya da na yankuna, Turkiyya na amfani da hanyoyin jinkai da na diflomasiyya, in ji Fahrettin Altun.

"Sakamakon nasarorin da aka samu a 'yan shekarun nan, ana bai wa Turkiyya girma a matakin kasa da kasa inda kuma ta taka rawa wurin magance matsalolin yankuna musamman a Gabas ta Tsakiya da yankin Caucasus," in ji shi.

Kan batun rikicin Isra'ila da Falasdinu, ya bayyana cewa matsayar da take da shi mai tare da mafita karkashin jagorancin Shugaba Erdogan, wadda ta mayar da hankali kan ayyukan jinkai ta tabbatar da hakan.

Kamar yadda aka nuna a matsalolin da suka shafi Ukraine da Karabakh da yankuna, a daidai lokacin da Jamhuriyar Turkiyya ta shiga karni na biyu, kasar ta zama babbar jagora a yankin da take," in ji Altun.

MAJIYA:AA
Rumbun Labarai
Abubuwan da suka kamata ku sani game da jirgin ruwan hakar mai na Cagri bey da ya isa Somalia
Erdogan ya gaya wa Pezeshkian cewa tattaunawar Amurka da Iran za ta samar da zaman lafiya mai ɗorewa
Yadda Ma'aikatar Tsaro ta Turkiyya take taimakawa wajen rage tunzurin yanki ta bayan fage
An kawar 'yanta'adda 3 kusa ta ofishin jakadancin Isra'ila a Istanbul: Ministan Cikin Gidan Turkiyya
Turkiyya ta ƙaddamar da shirin jigilar kaya ta Saudiyya saboda rufe Mashigar Hormuz
Israila na ci gaba da kawo cikas ga duk wani ƙoƙarin kawo ƙarshen yaƙin Iran: Erdogan na Turkiya
'Masu gurɓataccen ra'ayi': Me ya sa ƙaruwar gudunmawar Turkiyya a NATO ke kaɗa hantar Isra'ila?
Ruwa na maye gurbin mai a matsayin arziki mafi muhimmanci: Erdogan na Turkiyya
Turkiya ta doke Kosovo inda ta samu damar shiga gasar cin kofin duniya ta 2026
Zero Waste: Ƙarƙashin jagorancin Emine Erdogan, duniya ta tuna da Ranar Kawar da Shara
Shugaban Hukumar Leƙen Asiri ta Turkiyya ya yi gargaɗi kan rikicin Iran na iya zama na duniya
Kare gaskiya na da matuƙar muhimmanci a 'zamanin labaran ƙarya': Daraktan Sadarwa na Turkiyya
An fara taron Stratcom 2026 a Istanbul yayin da hankalin duniya ke ƙara tashi da yaƙin watsa labarai
Baya ga warware rikice-rikice, Turkiyya na sauya yadda al’amura ke gudana a duniya
Fidan na Turkiyya ya yi jerin tattaunawa da takwarorinsa kan kokarin kawo karshen yakin Iran
Ƙasashen Gulf za su iya ‘ɗaukar mataki’ kuma yaƙin Iran yana iya watsuwa: Babban jami'in Turkiyya
China ta yaba wa Turkiyya, Saudiyya, Qatar kan rawa a tsagaita wuta tsakanin Pakistan da Afghanistan
Shugaba Erdogan ya girmama nasarar 'Canakkale' a yaƙin duniya na ɗaya
Tallafin NATO ga Turkiyya zai gwada ƙarfin ƙawancensu yayin tashin hankalin Gabas ta Tsakiya: masana
An daƙile makami mai linzami na Iran a kan hanyarsa ta kutsawa Turkiyya