| Hausa
DUNIYA
3 MINTI KARATU
Majalisar tsaron Isra'ila ta amince a tsagita wuta da Hezbollah a Lebanon: kafofin watsa labaran cikin gida
Ana sa ran yarjejeniyar za ta fara aiki daga ranar Laraba.
Majalisar tsaron Isra'ila ta amince a tsagita wuta da Hezbollah a Lebanon: kafofin watsa labaran cikin gida
Isra'ila ta kashe fiye da mutune 3,768 a Lebanon tun daga watan Oktoban 2023. / Hoto: AA / Others

Majalisar tsaron Isra'ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a Lebanon, kamar yadda wata kafar yaɗa labarai ta cikin gida Channe 12 ta rawaito.

Ana sa ran yarjejeniyar za ta fara aiki daga ranar Laraba, kamar yadda rahoton ya bayyana a ranar Talata.

A bangre ɗaya kuma, Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ce a shirye yake ya yi aiki da yarjejeniyar ta tsagaita wuta a Lebanon, kuma zai “mayar da martani da ƙarfi idan Hezbollah ta saɓa yarjejeniyar.”

A wani jawabi da ya gabatar ta gidan talabijin, Netanyahu ya ce zai gabatar wa majalisar ministocinsa cikakken bayanin yarjejeniyar nan gaba a yau, bayan taƙaitacciyar majalisar tsaro ta amince da ita.

“Za mu aiwatar da yarjejeniyar, sannan za mu mayar da martani da ƙarfi idan aka saɓa ta. Za mu ci gaba da samun nasara tare,” a cewarsa.

Ya ƙara da cewa akwai dalilai uku da suka sa aka amince da yarjejeniyar – mayar da hankali kan Iran, da ƙara tara makamai da suka yi ƙasa da kuma bai wa sojoji dama su huta, sannan daga ƙarshe kuma a keɓe ƙungiyar gwagwarmaya ta Hamas.

'Abokan gana na Isra’ila ba su san ya kamata ba'

A wani ɓangaren kuma, a cikin wata sanarwa a ranar Talata, Firaministan Lebanon Najib Mikati ya buƙaci ƙasashen duniya “su ɗauki mataki nan take” don hana hare-haren Isra’ila, sannan “a aiwatar da tsagaita wuta nan take”.

Mikati ya ce irin hare-haren da Isra’ila ta kai Beirut ranar Talata “sun tabbatar da cewa abokan gaba na Isra’ila ba sa martaba kowace irin doka sannan ba su san ya kamata ba”.

“Muna kiran ƙasahen duniya su ɗauki mataki nan take don tsayar da miyagun hare-hare, sannan a tsagaita wuta nan take,” kamar yadda ya faɗa a wata sanarwa, wacce aka fitar gabanin Isra’ila ta ki hari tsakiyar yankin kasuwanci na Hamra.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Koriya ta Arewa ta yi alƙawarin kafa rundunar sojin ruwa mai amfani da makaman nukiliya
Faɗaɗa Yarjejeniyar Makka: Me Bangladesh za ta iya kawo wa ƙawancen?
Kotu a Las Vegas ta samu tsohon jagoran 'yandaba Duane 'Keffe D' Davis da laifi a kisan Tupac Shakur
Cizon sauron da suka shiga Jamus ta jirgin sama ya kashe ma'aikatan filin jirgi biyu
Tsananin zafi ya yi ajalin mutane 15,800 a Jamus a bazarar bana
Shugaban hukumar leƙen asiri ta Rasha ya tabbatar da ganawa da Shugaban CIA a Moscow
Ambaliya da zaftarewar ƙasa a Nepal sun yi ajalin gommai da ɓatar da ɗaruruwa a kusa da iyakar China
Trump ya gabatar da yarjejeniyar shekaru 30 ta haɗin gwiwar nukiliyar Saudiyya ga Majalisar Amurka
Mummunar guguwa ta katse wutar lantarki a gidaje 26,000 a kudu maso-gabashin Faransa
An kama mutane da dama bayan zanga-zangar ƙyamar Musulunci a Amurka
Fitaccen tsohon ɗanwasan Brazil Roberto Carlos ya musulunta - Rahotanni
Fafaroma ya yi kira a kawo karshen cin zarafin da Isra'ila ke yi wa Falasdinawa a Gabar Yamma
CIA ta yi shakkar iƙirarin da Isra'ila ta yi kan shirin halaka Trump bayan taron NATO: rahoto
Za a fara shari'ar wanda ake zargi da hannu a kashe Tupac Shakur a Amurka
‘Yan Bangladesh akalla 16 sun mutu sakamakon gobara a masana'antar yin kujeru ta Saudiyya
Gobarar daji a jihar Washington ta Amurka ta tilasta wa dubban mutane tserewa
Jirgin yaƙin Amurka samfurin F-35 ya faɗi kusa da wani sansanin soji
Tarayyar Turai ta yi kira da a zartar da umarnin Kotun ICC na kamo Netanyahu
Macron ya ce Faransa na fama da gobarar daji mafi muni da ba a taɓa ganin irinta ba
Turai na babbakewa: Me muka sani zuwa yanzu?