Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan da takwaransa na Mauritaniya Mohamed Ould Cheikh El Ghazouani sun tattauna dangantaka tsakanin ƙasashensu da batutuwa da suka shafi yanki, kamar yadda Ofishin Sanadrwar Turkiyya ya bayyana ranar Laraba.
A wata tattaunawa ta waya, Erdogan ya ce Turkiyya da Mauritaniya za su iya ƙarfafa dangatakarsu ta hanyar ɗaukar matakai ƙwarara a wasu fannoni, musamman ta cinikayya da noma da harkar kamun kifi da tsaro da masana’antar kare ƙasa , kamar yadda ofishin ya bayyana a shafin sada zumunta na Turkiyya NSosyal.
Shugaba Erdogan ya ƙara da cewa ƙasashen biyu za su ci gaba da aiki tare nan gaba domin ƙarfafa haɗin-kai a al’amuran ƙasa da kasa.
















