| Hausa
KASUWANCI
2 minti karatu
Ghana ta biya basussukan dala biliyan 1.47 na fannin makashi da ake bin ta
Ministan Kudi Forson ya ce fannin makamashin na cikin yanayi na rauni sosai a lokacin da Shugaba John Dramani Mahama ya karɓi ragamar mulki.
Ghana ta biya basussukan dala biliyan 1.47 na fannin makashi da ake bin ta
Zamanin tara bashi ba tare da tsari ba a bangaren makamashi ya ƙare, in ji Cassiel Ato Forson. / Reuters

Ghana ta biya adadin jimillar dala biliyan 1.47 a shekarar 2025 don warware tsoffin basussukan da ake bin ta a fannin makamashi da kuma dawo da samun garanti na Bankin Duniya a wannan sashen, in ji Ma'aikatar Kudi a wata sanarwa a ranar Litinin.

A cewar Ministan Kudi Cassiel Ato Forson, gwamnati ta biya duka basussukan dala miliyan 597.15 miliyan, ciki har da kuɗin ruwa, wanda aka karba ƙarƙashin Garanti na Bankin Duniya (Partial Risk Guarantee), wanda aka yi amfani da kuɗaɗen a shekarun baya.

Wannan biyan ya dawo da garantin, wanda yake da muhimmanci ga amincewar masu zuba jari a bangaren wutar lantarki na Ghana.

Minista Forson, a cikin bayanin da ya wallafa a X, ya ce bangaren makamashi yana cikin mawuyacin hali lokacin da Shugaba John Dramani Mahama ya karbi mulki a watan Janairun 2025, bayan shekaru na rashin biyan kuɗi ga iskar gas da ake samarwa ga bangaren wutar lantarki.

“Lokacin da Shugaba Mahama ya karbi mulki a watan Janairu 2025, an tilasta bangaren makamashi zuwa durƙushewa saboda shekaru da aka shafe na rashin biyan kuɗi ga gas ɗin da ake samarwa ga bangaren wutar lantarki daga bangaren Offshore Cape Three Points (OCTP).

“Saboda haka, an biya Garanti na Bankin Duniya na dala miliyan 500 miliyan gaba ɗaya wanda aka ciyo a ƙarƙashin gwamnatin da ta gabata,” in ji Forson.

'Iyakance taruwar bashi'

Haka zalika an bayyana cewa gwamnati ta biya takardun biyan gas da suka rage na kimanin dala miliyan 480 da ake bin ENI da Vitol saboda samar da wutar lantarki daga filin Offshore Cape Three Points (OCTP).

“Gwamnatin Ghana na tabbatar wa al'umma baki ɗaya, masu ruwa da tsaki a masana'antu, da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa cewa zamanin tara bashi da ƙin biyansa a bangaren makamashi ya ƙare,” in ji Forson.

Gwamnatin ta kuma biya kusan dala miliyan 393 a matsayin tsoffin basussukan da ake bin masu samar da wuta masu zaman kansu (IPPs), wanda hakan ya ƙara daidaita sashen.

Rumbun Labarai
Shigar kuɗaɗe daga waje cikin Nijeriya don zuba jari ta ƙaru da kusan kashi 90% a 2025 – Hukumomi
Hauhawar farashin mai ta janyo aiki daga gida da karatu daga nesa a wasu ƙasashen Asiya
Harin da aka kai wa 'yan kasuwar Ghana a Burkina Faso ya sa farashin tumatur ya tashi
Naɗin 'ya'yan Dangote mata uku a manyan muƙamai: Sabon babi a tsarin gado na kasuwancin iyali
China za ta soke karɓar harajin fitar da kayayyaki daga ƙasashen Afirka 53
Me ya sa farashin zinare ke tashi a lokacin rikicin siyasa a duniya?
Gwamnatocin Afirka sun juya ga tsarin Bankin Musulunci bayan nasarar Sukuk a Benin
Ana sa ran kasuwanci tsakanin Turkiyya da Nijeriya ya kai dala biliyan 10 saboda sabbin yarjeniyoyi
Afrika na amfani da tagomashin da zinari yake samu don ƙara ƙarfin arziƙinta
Trump ya ce Amurka za ta karɓi gangar ɗanyen mai miliyan 50 daga Venezuela
Kamfanin Dangote ya yi watsi da ikirarin rufe matatar mansa
Me ya sa hanyoyin teku da aka toshe ke tayar da kura a Gabashin Afirka?
ECOWAS za ta cire harajin tafiye-tafiyen jiragen sama tsakanin ƙasashen Yammacin Afrika a 2026
Manyan ƙere-ƙeren fasaha na Afirka da suka yi tasiri a duniya
Abu biyar da ya kamata ku sani kan Taron G20 na farko a Afirka
An cire Nijeriya daga jerin kasashen da ake sa wa ido kan safarar kudade ba bisa ka'ida ba a duniya
Bai kamata kasuwanci da Afirka ya zama buƙatar ɗiban ma’adanai ba: Ministan Nijeriya Tuggar
Jamhuriyar Nijar ta kafa cibiyar tsaron intanet
Kamfanin simintin Dangote ya fara aiki a ƙasar Ivory Coast
Ana hasashen mambobin OPEC+ za su ƙara yawan fetur ɗin da suke fitarwa yayin da farashinsa ke karewa