Sakataren Harkokin Wajen Amurka Rubio na matsa wa UAE lamba domin tsagaita wuta a Sudan

Marco Rubio ya buƙaci Abu Dhabi da ta taimaka domin dakatar da yaƙin da ake yi a Sudan, tare da gargaɗin cewa dole ne a dakatar da bai wa mayaƙan RSF makamai.

By
Yayin da yake magana da 'yan jarida a ranar Laraba, Rubio ya ce Washington na yin 'duk abin da za ta iya' don kawo ƙarshen rikicin.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio ya jaddada buƙatar ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta domin ayyukan jinƙai a Sudan.

Ya bayyana haka ne a wata tattaunawa ta waya da Ministan Harkokin Wajen Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa Sheikh Abdullah bin Zayed Al Nahyan, 'yan kwanaki bayan da ya yi gargaɗi kan cewa ana buƙatar ɗaukar mataki don katse hanyoyin shigar da makamai ga RSF.

Mai magana da yawun Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka Tommy Pigott ya ce Rubio ya 'jaddada muhimmancin cim ma yarjejeniyar domin ayyukan jinƙai a Sudan a lokacin da suke tattaunawa ta waya.

Sojojin Sudan sau da yawa suna zargin UAE da samar da makamai da kuma bayar da sojojin haya ga RSF, zarge-zargen da ƙwararrun Majalisar Ɗinkin Duniya da wasu 'yan majalisar Amurka suka ga alamar akwai ƙamshin gaskiya a ciki.

Yayin da yake magana da 'yan jarida a ranar Laraba, Rubio ya ce Washington na yin 'duk abin da za ta iya' don kawo ƙarshen rikicin.

'Akwai bukatar a yi wani abu don katse shigowar makamai da tallafin da RSF ke samu yayin da suke ci gaba da ƙarawa gaba,' in ji shi.

An tambaye shi ko UAE na cikin ƙasashen da ke samar da makamai, sai Rubio ya ƙi ambata sunanta a fili amma ya ƙara da cewa: 'Mun san waɗanne ɓangarori ke da hannu... shi ya sa suke daga cikin Quad, tare da wasu kasashen da ke da hannu. Zan iya gaya muku daga matakin kololuwa na gwamnatimmu cewa ana gabatar da hujjoji kuma ana matsa wa ɓangarorin da abin ya shafa. Dole ne a dakatar da wannan.'

Ya kuma ce ba ya ƙaryata yiwuwar ayyana RSF ƙungiyar ta'addanci idan hakan zai taimaka domin kawo ƙarshen rikicin.

MDD ta ƙaddamar da bincike, Turkiyya ta nemi a dakatar da fada

Wannan lamari ya faru ne bayan Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan’adam ta Majalisar Dinkin Duniya a ranar Jumma'a ta amince da wani kudiri wanda ya kafa wata tawagar bincike don gano take hakkin bil'adama a al-Fasher, babban birnin Arewacin Darfur, wanda RSF ta kwace.

Majalisar ta umarci masu bincike da su gano waɗanda ake zargi da hannu a ta'asar domin a gurfanar da su a gaban shari'a.

Turkiyya, ta hanyar jawabi da wakilinta na dindindin ya yi a Geneva, Burak Akçapar, ta bukaci a dakatar da yaƙi nan take a al-Fasher da kewaye, a kawo ƙarshen hare-hare kan farar-hula, tare da samar da hanyoyin jinƙai yayin da tashin hankali ke yaɗuwa a Darfur da Kordofan.