| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Aƙalla mutane 518 ne suka mutu a zanga-zangar bayan zaɓe a Tanzania: Bincike
Kwamitin binciken ya ce ba a tabbatar da zarge-zargen binne mutane da yawa a waje guda ba, kuma hotunan da aka yaɗa a intanet an samar da su ne ta hanyar amfani da ƙirƙirarriyar basira (AI).
Aƙalla mutane 518 ne suka mutu a zanga-zangar bayan zaɓe a Tanzania: Bincike
FILE PHOTO: 'Yan sanda do sojoji sun kalubalanci masu zanga-zangar. / AP / AP

Kwamitin bincike da gwamnati ta kafa a ranar Alhamis ya ce rikicin zaɓe a ƙasar Tanzania a bara ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutane 518.

An ayyana shugaba Samia Suluhu Hassan a matsayin wadda ta lashe zaɓen ranar 29 ga Oktoba da kashi 98 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa bayan da aka hana manyan 'yan adawa tsayawa takara.

Amma zaɓen ya haifar da zanga-zanga a faɗin ƙasar tsawon kwanaki da dama.

'Yan adawa da ƙungiyoyin addini sun ce an kashe dubban mutane, tare da rahotannin cewa an samu kaburburan da aka binne mutane da yawa da ƙwace gawarwaki daga ɗakunan ajiyarsu na asibiti.

Gwamnati ba ta bayar da wani adadi na waɗanda suka mutu ba har zuwa ranar Alhamis, kuma kwamitin ya gano cewa "ba za a iya tabbatar da zargin wanzuwar kaburburan da aka binne mutane da yawa ba".

‘Hotuna da aka ƙirƙira’

"Jimillar mace-macen da aka samu sakamakon babban zaɓen sun kai 518, waɗanda 490 daga ciki maza ne," in ji Mohamed Chande Othman, shugaban kwamitin da Shugaba Saluhu Hassan ta kafa, amma ya ce adadin "ba na ƙarshe ko kuma kammalalle ba ne".

"Hotunan da aka yaɗa a intanet, wasu daga cikinsu na gaske ne, yayin da wasu... an ƙirƙire su ne ta amfani da fasahar zamani ta AI," in ji Othman.

Katsewar intanet a lokacin da kuma bayan zaɓen ya rikitar da ƙoƙarin tabbatar da girman tashin hankalin.

'Yan adawa sun ce binciken "ba zai iya zama mai zaman kansa ko kuma marar son kai ba, musamman a yanayin da gwamnati ke kan gaba wajen aikata laifukan da ake bincike a kansu".

Tashin hankalin ya haifar da suka mai tsanani daga masu sa ido na Afirka, inda Tarayyar Afirka ta ce zaɓen bai bi ƙa'idojin zaɓen dimokuraɗiyya ba."

Rumbun Labarai
Morocco ta saki magoya bayan Senegal da aka ɗaure kan hargitsin wasan ƙarshe na AFCON
Ziyarar Afirka: Fiye da mutum 500,000 ake sa ran sun halarci taron ibada na Fafaroma Leo a Kamaru
Yara mata ne suka fi cutuwa daga yaƙin Sudan da aka manta da shi
Fafaroma Leo ya nufi Kamaru ƙasa ta biyu a ziyararsa ta Afirka
Yaƙi ya jefa fiye da kashi 70 cikin 100 na 'yan ƙasar Sudan cikin talauci, in ji MƊD
Yadda yakin Iran ke shafar tattalin arziki, yanki da siyasar Afirka
Za a cim ma yarjejeniyar bututun gas na Nijeriya-Maroko kan biliyan $25 a bana: Jami'i
Fafaroma Leo ya fara ziyararsa ta farko zuwa Afirka
Matsalar yunwa a Sudan: Miliyoyin mutane na cin abinci sau ɗaya a rana
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Jamhuriyar Benin
Shugaban ƙasar Djibouti Guelleh ya sake yin nasara karo na shida
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Djibouti inda Guelleh da ke mulki ke neman wa'adi na shida
Daga hanyoyin mulkin mallaka zuwa na korar mutane: Afirka da siyasar korar baƙi daga wata ƙasa
Yadda ajujuwan Afirka ke fuskantar jarrabawa mafi tsauri a duniya
Kamaru ta ce ‘yan kasarta 16 sun mutu yayin taya Rasha yaki da Ukraine
Dalilin da ya sa Kenya da Ethiopia suka zama manyan masana'antun furanni a duniya
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 15 a Angola
Senegal ta haramta wa jami'an gwamnati tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa ƙasashen waje
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina