| Hausa
WASANNI
1 minti karatu
Riyad Mahrez ya yi ritaya daga tawagar Algeria bayan fitar da su daga Kofin Duniya
Kafin ritayar tasa, Riyad Mahrez ya jagoranci ƙasarsa wajen lashe kofin ƙasashen Afirka na AFCON a 2019, wanda shi ne karo na biyu da ƙasar ta lashe.
Riyad Mahrez ya yi ritaya daga tawagar Algeria bayan fitar da su daga Kofin Duniya
Riyad Mahrez ya yi ritaya daga tawagar Algeria bayan fitar da su daga Kofin Duniya / Reuters

Tauraron ɗanwasan Algeria, Riyad Mahrez ya sanar da ritayarsa daga buga wa ƙasarsa bayan an fitar da su daga gasar Kofin Duniya da ke gudana a Amurka, Canada, da Mexico.

Switzerland ce ta fitar da Algeria a zagayen ‘yan-32, inda ta doke ta da ci 2-0 ta hannun Breel Embolo da Dan Ndoye.

Mai shekaru 35, Mahrez wanda tsohon ɗanwasan Manchester City da Leicester na Ingila ne, ya kwashe shekaru 12 yana buga wa ƙasar inda ya buga wasanni 119.

A bayanin da ya yi bayan wasan, Mahrez ya ce wannan ne karo na ƙarshe da zai buga wa tawagar ƙasarsa wasa.

"Wannan ne karona na ƙarshe, hatta a tawagar ƙasa. Wannan ne wasana na ƙarshe," in ji Mahrez.

Kafin ritayar tasa, Riyad Mahrez ya jagoranci ƙasarsa wajen lashe kofin ƙasashen Afirka na AFCON a 2019, wanda shi ne karo na biyu da ƙasar ta lashe.

A yanzu yana buga wa ƙungiyar Al-Ahli ta Saudiyya tun shekarar 2023.