| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
An yi wa jagoran 'yan adawa na Guinea Bissau ɗaurin talala
Wata kotun soji a ƙasar Guinea Bissau ta ba da umarni ranar Alhamis cewa a tsare jagoran 'yan adawa Domingos Simoes Pereira a gida bayan an yi masa tambayoyi game zargin kitsa yi wa gwamnati juyin mulki.
An yi wa jagoran 'yan adawa na Guinea Bissau ɗaurin talala
Rahotanni sun ce an tsare jagoran 'yanadawa na Guinea Bissau Domingos Simoes Pereira a gida / AA

Wata kotun soji a ƙasar Guinea Bissau ta ba da umarni ranar Alhamis cewa a tsare jagoran ‘yanadawa a ƙasar Domingos Simoes Pereira a gida, bayan an sake yi masa tambayoyi game da zarge-zargen kitsa juyin mulki ga gwamnati, kamar yadda lauyansa ya bayyana .

An tsare Pereira, shugaban jam’iyyar PAIGC, a lokacin da sojoji suka yi wa Shugaba Umaro Sissoco Embalo juyin mulki ranar 26 ga watan Nuwamban shekarar 2025.

An sake shi a ƙarƙshin sharaɗin yi masa ɗaurin talala a watan Janairu, amma an zarge shi da hannu a yunƙurin juyin mulki biyu da aka yi a baya, ɗaya a shekarar 2023 ɗaya kuma a watan Oktoban shekarar 2025.

Jami’an tsaro da yawa ne suka kewaye kotun da Pereira ya gurfana a gabanta ranar Alhamis.

'Bai san kome game da shi ba'

Joao Paulo Indeque, ɗaya daga cikin lauyoyin Pereira, ya sanar da manema labarai cewa mutumin da yake karewa ya amsa duk tambayoyin alƙali.

"Domingos Simoes Pereira ba shi da hannu a ko wane yunƙurin zagon ƙasa ga gwamnatin da ke bisa tsarin mulki . Bai san kome game da shi ba, muna da tabbacin hakan," kamar yadda Indeque ya bayyana.

Janar Horta N'Tam ne ke jagorantar gwamnatin riƙon ƙwarya da ke mulki a Guinea Bissau a halin yanzu.

Rumbun Labarai
Jami'an tsaro a Afirka ta Kudu sun kama masu haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba fiye da 200
Ƙawancen tsaro na Turkiyya da Afirka na haɓaka a tsarin duniya da ke sauyawa
Jami’an leken asiri sun lalata yunƙurin ‘yan ta’addan Daesh na kai hari a garuruwan Morroco bakwai
'Yansandan Afirka Ta Kudu sun ce mutuwar ɗan Nijeriya ba ta da alaƙa da tashin hankalin ci-rani
MDD ta yi gargaɗin cewa hare-haren RSF na iya mayar da birnin Al-Obeid na Sudan kamar Al-Fasher
Rikicin diflomasiyya ya kaure tsakanin Ghana da Afirka ta Kudu kan mutuwar ɗan Ghana
Burkina Faso, Mali da Nijar sun gabatar da sanarwar ficewa daga ICC, in ji kotun
Sojojin Mali sun raka motocin dakon mai da abinci 940 zuwa Bamako saboda fargabar harin ta'addanci
Sojojin Burkina Faso sun ce sun kashe 'yanta'adda fiye da 400 a wani hari da suka daƙile
An gurfanar da ɗalibai mata takwas a kotu a Kenya kan zargin kisan abokan karatunsu a gobara
Yadda Nijeriya ke fama da hauhawar farashin gas din girki
MDD ta yi gargaɗin cewa cutar Ebola na iya jefa kusan mutane miliyan 1 cikin talauci a DRC
Afirka ta Kudu ta mai da fiye da mutum 25000 kasashensu kafin wa'adin 30 ga Yuni na masu ƙyamar baƙi
Yadda abinci ke yin kisan mummuƙe a Afirka
Burkina Faso ta kawo ƙarshen dangantakar diflomasiyya da Faransa
Fiye da mutum 1,400 sun tsere daga jihar North Darfur ta Sudan a yini ɗaya yayin da ake zafafa yaƙi
Nijeriya da ƙasashe 4 sun ƙaddamar da sabuwar hukuma kan hanyar Abidjan zuwa Lagos ta $16bn
Nijar ta gabatar da takardar buƙatar ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya, ICC
An ci gaba da amfani da cin zarafin jinsi a matsayin makamin yaƙi a Sudan: MDD
Manyan Jami’o’in Afirka: Afirka ta Kudu ce ke kan gaba a awon matsayi na baya bayan nan