| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Mutum 28 sun mutu a Ethiopia bayan wata bas ta faɗa a kwazazzaɓo
Hukumomin cikin gidan suna nuna yadda wurare masu yawan kwane-kwane da rashin mayar da hankali na direbobi ke haddasa hatsura da ke janyo mace-mace da yawa.
Mutum 28 sun mutu a Ethiopia bayan wata bas ta faɗa a kwazazzaɓo
Mutum 28 sun mutu a Ethiopia bayan wata bas ta faɗa a kwazazzɓo / AFP

Aƙalla mutum 28 ne suka mutu a lokacin da wata bas ta tsunduma cikin wani kwazazzabo a yankin Amhara na Ethiopia, kamar yadda kafar watsa labarai mallakar lardin Amhara ta ruwaito ranar Litinin, tana mai ambato majiyar ‘yansanda.

Bas ɗin ta kasance tana tafiya ne daga Dessie zuwa babban birnin ƙasar , Addis Ababa, a lokacin da hatsarin ya auku , in ji kafar watsa labaran .

"Kawo yanzu , mutum 28 sun rasa rayukansu , yayin da da yawa suka ji ƙanana da munanan raunuka," kamar yadda kafar ta ambato rundunar ‘yansanda tana cewa.

Ana yawan samun haɗurar kan hanya a Ethiopia, inda tsarin tuƙi ke da rauni kuma ba a kula da motoci da yawa yadda ya kamata.

Rundunar ‘yansanda masu ba da hannu na yankin da masu magana da yawun rundunar suna nunawa akai-akai yadda yanayi mai kwane-kwane da yawa da rashin mayar da hankali na direbobi ke haddasa haɗura da ke janyo yawan mace-mace.

A ranar 11 ga watan Fabrariru na shekarar 2025, aƙalla mutum 26 sun mutu yayin da saura 45 suka ji rauni a wani hatsari na kan hanya a yankin Oromia na Ethiopia, kamar yadda kafafen watsa labarai na cikin gida suka ruwaito.

Kuma a shekarar 2024, aƙalla mutum 71 sun mutu a kudancin yankin Sidama bayan wata babbar mota ta tsunduma cikin wani kogi.

Rumbun Labarai
Gwamnatin Mali ta tabbatar da kashe sojoji 30 a wani harin ta'addanci a arewacin ƙasar
Aikin matatar man Dangote zai ci gaba a gaɓar tekun  Kenya, a cewar Shugaba Ruto
Afirka ta sami tallafin $900m domin faɗaɗa fasahar girki na zamani mara gurɓata muhalli
Rasha na son ƙarfafa alaƙa da Ƙawancen Ƙasashen Sahel (AES) - Lavrov
Sojojin Sudan sun ƙwace ƙauyen Al-Kurmuk bayan arangama da dakarun RSF
Jami'an tsaro a Afirka ta Kudu sun kama masu haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba fiye da 200
Ƙawancen tsaro na Turkiyya da Afirka na haɓaka a tsarin duniya da ke sauyawa
Jami’an leken asiri sun lalata yunƙurin ‘yan ta’addan Daesh na kai hari a garuruwan Morroco bakwai
'Yansandan Afirka Ta Kudu sun ce mutuwar ɗan Nijeriya ba ta da alaƙa da tashin hankalin ci-rani
MDD ta yi gargaɗin cewa hare-haren RSF na iya mayar da birnin Al-Obeid na Sudan kamar Al-Fasher
Rikicin diflomasiyya ya kaure tsakanin Ghana da Afirka ta Kudu kan mutuwar ɗan Ghana
Burkina Faso, Mali da Nijar sun gabatar da sanarwar ficewa daga ICC, in ji kotun
Sojojin Mali sun raka motocin dakon mai da abinci 940 zuwa Bamako saboda fargabar harin ta'addanci
Sojojin Burkina Faso sun ce sun kashe 'yanta'adda fiye da 400 a wani hari da suka daƙile
An gurfanar da ɗalibai mata takwas a kotu a Kenya kan zargin kisan abokan karatunsu a gobara
Yadda Nijeriya ke fama da hauhawar farashin gas din girki
MDD ta yi gargaɗin cewa cutar Ebola na iya jefa kusan mutane miliyan 1 cikin talauci a DRC
Afirka ta Kudu ta mai da fiye da mutum 25000 kasashensu kafin wa'adin 30 ga Yuni na masu ƙyamar baƙi
Yadda abinci ke yin kisan mummuƙe a Afirka
Burkina Faso ta kawo ƙarshen dangantakar diflomasiyya da Faransa