| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Ana zargin giya ta kashe mutum 49 a Jihar Ondo da ke kudancin Nijeriya
Hukumomin Jihar Ondo na zargin cewa gubar methanol ce ta haddasa mutuwar mutanen, daga wata giya da ake hadawa a gargajiyance wadda aka fi sani da “Monkey Tail”.
Ana zargin giya ta kashe mutum 49 a Jihar Ondo da ke kudancin Nijeriya
Methanol wani nau’in barasa ne mai matuƙar guba wanda zai iya haddasa mummunar illa, makanta, lalacewar gabobin jiki da kuma mutuwa idan aka sha.

Akalla mutane 49 sun mutu, yayin da wasu 182 ke kwance a asibitoci bayan zargin shan wata giya a jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Nijeriya, kamar yadda kwamishinan lafiya na jihar ya bayyana.

An fara bayar da rahoton wannan matsalar lafiya ta gaggawar a ranar 5 ga Satumba, lokacin da hukumomi suka ce mutane 29 sun mutu cikin mako guda bayan shan barasar da ake zargin ta gurɓace. Kwamishinan Lafiya na Jihar Ondo, Banji Ajaka, ya ce zuwa ranar Jumma’a adadin wadanda suka mutu ya karu zuwa 49.

Hukumomin Jihar Ondo na zargin cewa gubar methanol ce ta haddasa mutuwar mutanen, daga wata giya da ake hadawa a gargajiyance wadda aka fi sani da “Monkey Tail”. Lamarin ya sake nuna haɗarin shaye-shayen barasa marasa ingantaccen tsari, waɗanda ake yawan amfani da su a wasu sassan Nijeriya saboda arha da sauƙin samuwa.

“Yanayin rashin lafiyar da kuma bayanan da aka samu kan yadda mutanen suka sha abin ya haifar da babbar zargin cewa sun sha wani sinadari mai guba da ke cikin barasar. Sai dai har yanzu ba mu samu shaidar ɗakin gwaje-gwaje ba,” in ji Ajaka a cikin wata sanarwa.

Ya ce wadanda abin ya shafa sun nuna alamomi da suka haɗa da ciwon kai, ciwon jiki, wahalar numfashi, fita daga hayyaci, da kuma makanta.

“Wannan abu ya faru cikin gaggawa. Da zarar sun sha, gwargwadon yawan abin da suka sha, ƙoda na iya daina aiki, idanu su makance, sannan kwakwalwa ta lalace,” in ji Ajaka.

Methanol wani nau’in barasa ne mai matuƙar guba wanda zai iya haddasa mummunar illa, makanta, lalacewar gabobin jiki da kuma mutuwa idan aka sha.

Rundunar ‘yansanda ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da hannu a lamarin, yayin da hukumomi ke ci gaba da bincike domin gano tushen barasar da ake zargin ta gurɓace.

Har yanzu hukumomi ba su tabbatar ta hanyar gwajin dakin gwaje-gwaje cewa methanol ce ta haddasa mutuwar mutanen ba.

 

 

Rumbun Labarai
Dakarun Nijeriya sun kubutar da mutane 31 da aka yi garkuwa da su a jihohin Katsina da Kebbi
Rundunar sojin Nijeriya 'ta kashe ‘yanta’addan Boko Haram da ISWAP fiye da 1000 a shekara ɗaya'
Samun ɗa namiji magaji ba ya gabana - Aliko Dangote
Rundunar 'yansandan Nijeriya ta yi gargaɗi game da yiwuwar kai hare-hare makarantu da wuraren ibada
Ana zargin ‘yanta’adda da kashe aƙalla mutum 13 a wasu hare-hare a Jihar Filato ta Nijeriya
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 262, sun kuma ceto 27 da aka yi garkuwa da su
An sace malamai shida da suka je taron addu’ar APC a Zamfara
Gwamnatin Nijeriya ta yi Allah wadai da kisan 'yan ƙasarta biyu a Afirka ta Kudu
FBI ta nemi haɗin kan EFCC don gudanar da bincike kan zargin karkatar da kuɗaɗen tallafin Amurka
Majalisar Dokokin Nijeriya ta dakatar da ziyarar aiki zuwa Afirka ta Kudu
Tinubu ya bai wa kowace 'yar tawagar ƙwallon kwandon Nijeriya dala dubu ɗari-ɗari
Mutum 511 sun kamu da cutar mashaƙo a Jihar Yobe a Nijeriya
Amurka ta aika sabbin kayayyakin soji Nijeriya
Zaben Nijeriya na 2027: Matakan Tinubu na rage talauci da alƙawarin Atiku na mayar da tallafin fetur
Jakadan Nijeriya ya ziyarci ’yan kasar 198 da ke gidan yari a Indiya
Mutane da dama sun mutu yayin da wasu ke asibiti bayan sun sha wani maganin gargajiya a jihar Ondo
Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya ta kama wasu mutane da kudade da ake zargin kuɗin fansa ne
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum biyu kan zargin kashe Danshagamu a Kano
Nijeriya ta naɗa sabon kwamandan yaƙi da ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram
NEMA ta karɓi ’yan Nijeriya 180 da aka mayar da su gida daga Libya