| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
An daure wani babban dansiyasar Ghana tsawon shekaru 20 saboda hakar ma'adanai ba bisa ka'ida ba
Ranar Litinin wata kotu a Ghana ta ɗaure wani ɗansiyasa ɗan-adawa tsawon shekaru 20 bayan ta same shi da laifin haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba.
An daure wani babban dansiyasar Ghana tsawon shekaru 20 saboda hakar ma'adanai ba bisa ka'ida ba
Wata kotu a Ghana ta yanke wa Bernard Antwi-Boasiako hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari a ranar 20 ga Yuli, 2026, saboda hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba.

Wata kotu a Ghana ta yanke hukuncin ɗaurin shekaru 20 ga Bernard Antwi-Boasiako, wani ɗansiyasa mai faɗa-a-ji, bayan ta same shi da laifin haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba.

Wannan hukuncin da aka yanke ranar Litinin ya zamo mutum mafi fice da aka samu da laifi sakamakon irin wannan laifi a yaƙi da ake da laifuka irin waɗannan.

Kasar mai arziƙin zinari tana fafutukar yaƙi da haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba, abin da ake kira ƙasar da 'galamsey', wadda matsala ce ta gurɓatar muhalli, da barazana ga samar da cocoa da rashawa a siyasa waɗanda suka yaɗu a 'yan shekarun nan.

Hukumomi sun ce ayyukan Galamsey sun halaka gandun daji, sun gurɓata rafuka da koguna, kuma suna janyo wa ƙasar asarar kimanin dalar Amurka biliyan 2 duk shekara.

Babbar kotun a Accra ta samu Bernard Antwi-Boasiako, shugaban jam'iyyar adawa ta New Patriotic Party (NPP), reshen Ashanti, da duka tuhume-tuhume shida da aka gabatar kansa.

'Tuhumar ba a musanta ba'

Laifukan sun haɗa da ba da haƙƙin haƙar ma’adanai ba bisa doka ba, da kuma taimakawa ayyukan haƙar ma'adinai da gangan ba tare da lasisi ba a wuraren haƙar zinari.

An yanke masa hukuncin ne bayan cafke wasu ma'aikatan haƙar ma'adinai a watan Afrilun 2025, da kuma ƙwace na'urorin tonon ƙasa, makamai, da tsabar kuɗi a wani samame da 'yansanda suka kai kan wuraren haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba.

“Ba su musanta Tuhumar ba. Wanda ake zargin ya amsa cewa ba a samu amincewar ma’aikatar gwamnati ba,” in ji alƙali Audrey Kocuvie-Tay.

Hukuncin na shekaru 20 yana cikin zangon hukuncin da dokokin ƙasar ta Afirka ta Yamma suka tanada, tsakanin shekaru 15 zuwa 25.

'Haƙƙin ɗaukaka ƙara'

Antwi-Boasiako, wanda aka fi sani da Chairman Wontumi, mutum ne sananne a NPP, jam'iyyar da ta mulki Ghana daga 2017 zuwa 2025, kafin ta rasa mulki a hannun jam'iyyar National Democratic Congress ƙarƙashin Mahama.

Da dama cikin jigajigan NPP, ciki har da tsohon Ministan Kuɗi, Ken Ofori-Atta, sun fuskanci bincike ko shari'o'i tun bayan dawowar NDC kan mulki.

Gwamnatin na cewa binciken da shari'o'in suna dogara ne kan hujjoji kuma ba su da alaƙa da siyasa.

Antwi-Boasiako na da haƙƙin ɗaukaka ƙara dangane da samunsa da laifin da kuma hukuncin da aka yanke masa.