| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Sojin Nijeriya sun halaka ‘yanta’adda 50, sun yi asarar dakaru biyu yayin daƙile harin ISWAP a Yobe
Harin ya faru ne da sanyin safiyar Alhamis, 8 ga watan Mayun 2026, lokacin da ‘yanta’addan suka kai farmaki daga sassa daban-daban a cikin duhun dare.
Sojin Nijeriya sun halaka ‘yanta’adda 50, sun yi asarar dakaru biyu yayin daƙile harin ISWAP a Yobe
Wasu daga cikin makaman da sojojin Nijeriya suka ƙwato / Nigerian army

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta yankin Arewa maso Gabas Operation HADIN KAI sun dakile wani harin haɗin gwiwa da mayaƙan ISWAP suka kai hedikwatar Brigade ta 27 da kuma shingen bincike na Buni Gari a Jihar Yobe, inda aka kashe aƙalla ‘yanta’adda 50 a yayin artabun.

Harin ya faru ne da sanyin safiyar Alhamis, 8 ga watan Mayun 2026, lokacin da ‘yanta’addan suka kai farmaki daga sassa daban-daban a cikin duhun dare.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na Operation HADIN KAI, Laftanar Kanal Sani Uba ya fitar, ya ce ‘yanta’addan sun fara kai hari daga ɓangaren yamma kafin su ƙara tura mayaƙa daga kudanci ta hanyar Ganinga Junction sannan daga kudu maso yamma domin kewaye dakarun.

Sai dai ya ce dakarun sun tsaya tsayin daka tare da mayar da martani da manyan makamai da dabarun yaƙi da suka tilasta wa maharan ja da baya cikin ruɗani.

Operation HADIN KAI ta kuma tabbatar da rasuwar sojoji biyu a yayin artabun, inda ta bayyana su a matsayin jarumai da suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasa.

Sojojin sun ce an gano gawarwakin ‘yanta’adda guda 10 a kusa da sansanin, yayin da rahotannin sirri suka nuna cewa an gano fiye da gawarwaki 20 a hanyoyin da suka bi wajen tserewa ta yankunan Gashua, Azare da Kamuya.

Rundunar sojin sama ta OPHK ma ta kai hare-haren sama kan ‘yanta’addan da ke guduwa, inda ta kashe kusan mayaƙa 20.

Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogi ƙirar AK-47 guda takwas, bindigogin GPMG guda biyu, roka guda biyu, bama-baman RPG, jigidar harsasai, da kuma kwalaben na’urorin tayar da bama-bamai na IED guda uku.

Sojojin sun kuma bayyana cewa wasu motocin kariya daga hare-haren bama-bamai na MRAP da motocin yaƙi sun lalace yayin musayar wuta, yayin da jami’an da suka jikkata ke samun kulawar lafiya kuma suna cikin yanayi mai kyau.

Rundunar ta ƙara da cewa dakaru tare da haɗin gwiwar jami’an sa-kai na ci gaba da gudanar da sintiri da bincike a yankin domin farautar ‘yan ta’addan da suka tsere tare da hana su sake haɗuwa.

Rumbun Labarai
An kama mutumin da ake zargi da kirkirar muryar bogi ta Shugaba Tinubu ta hanyar AI
Nijeriya za ta kwashe 'yanƙasarta fiye da 1,000 daga Afirka Kudu saboda matsalar ƙyamar baƙi
'Yanbindiga sun yi garkuwa da ɗalibai 7 daga wata makaranta a Jihar Zamfara ta Nijeriya
Kotu a Nijeriya ta yanke wa mutum huɗu hukuncin kisa kan harin Cocin Owo na 2022
'Yansanda sun gano wajen ƙera bindigogi a arewa maso gabashin Nijeriya‎
'Yan Nijeriya 'yan ci-rani 65,500 da suka makale a ƙasashen waje aka ceto cikin shekaru tara
Matatar Dangote ta ce tana da isasshen man jirgi da za ta iya wadatar da bukatun “duniya"
Farashin man fetur a Nijeriya ya tashi da kashi 643% a cikin shekaru uku — Rahoto
Wike ya ce kiwon shanu a cikin birnin Abuja batu ne na tsaron ƙasa
Tinubu ya ba da damar ɗaukar jami'an tsare dazuka 1,000 sakamakon garkuwa da ɗaliban jihar Oyo
Tsayar da Obi ɗan takarar NDC ya sake share fagen fafatawar manyan 'yan takara uku a Nijeriya
NAHCON ta ba da umarnin bincike kan wani abinci da mahajjata suka ƙi ci kan 'rashin inganci'
Masu tayar da ƙayar baya 30,000 na rura wutar rashin tsaro a Nijeriya - Rahoton Amurka
'Yanbindiga sun yi garkuwa da mutum 10 tare da kona gidan wani sarki a jihar Kwara a Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yanta’adda 12 da ƙwato makamai a Borno
Wa zai fafata da Tinubu? Jam'iyyun siyasar Nijeriya na zaɓen fitar da 'yan takarar shugabancin ƙasar
Kotu ta soke jadawalin INEC game zabukan fitar da gwani da tsayar da 'yantakara na 2027
Tinubu ba shi da shirin sauya sunan Nijeriya ko soke shari'ar Musulunci a arewa – Fadar gwamnati
Hukumar Alhazan Nijeriya ta kammala jigilar maniyyatan ƙasar zuwa Saudiyya
Fitaccen Fasto a Nijeriya ya ba magoya bayan Arsenal haƙuri kan 'saƙon wahayin ƙarya' da ya isar