| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Saudiyya ta ce wasu jirage marasa matuƙa da aka aika daga Iraƙi sun kai hari kan wani bututun mai
Saudiyya ta ce jiragen sama marasa matuƙa da aka aika daga Iraƙi sun kai hari kan bututun da ke jigilar mai daga Gabashin Saudiyya zuwa Yammaci, lamarin da ya kai ga rufe bututun.
Saudiyya ta ce wasu jirage marasa matuƙa da aka aika daga Iraƙi sun kai hari kan wani bututun mai
Riyadh ta ce harin da aka kai kan bututun mai "ya yi sanadin jikkatar mutane da barna". / AA Archive

Saudiyya ta ce jiragen sama marasa matuƙa da aka aika daga Iraƙi sun kai hari kan bututun da ke jigilar mai daga Gabashin Saudiyya zuwa Yammaci, lamarin da ya kai ga rufe bututun, yayin da Bagadaza ta yi maraba da shawarar Riyadh ta dakatar da mayar da martani.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Saudiyya ta yi Allah wadai a ranar Jumma’a da “kai hari kan bututun mai na East–West a yankunan Riyadh da Madina ta hanyar jiragen sama marasa matuƙa da dama da suka fito daga Iraƙi, lamarin da ya haddasa jikkatar mutane da lalata kadarori.”

“An rufe da bututun a matsayin matakin kariya, kuma hare-haren sun jikkata wasu mutane,” kamar yadda wani jami’in ma’aikatar makamashi ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Saudiya (SPA) a baya.

Ma’aikatar Harkokin Wajen ta ce, “Bisa buƙatar Firaministan Iraƙi... (Riyadh) ta zaɓi kada ta mayar da martani a wannan mataki, tare da tallafa wa ƙoƙarin gwamnatin Iraƙi ... na hana hare-haren da ake ƙaddamarwa daga Iraƙi kan Masarautar da ƙasashen makwabta.”

Sai dai ta jaddada cewa Saudiyya “tana da haƙƙin ɗaukar dukkan matakan da suka dace domin kare ikon mulkinta, tsaronta, wuraren aikinta,” da kuma mazaunanta.

Saudiya ta ce hare-haren da suka faru a safiyar Alhamis sun jikkata mutane da dama.

Iraƙi ta yi maraba da shawarar Saudiyya ta dakatar da mayar da martani.

Ta yi Allah wadai da duk wani hari da ke barazana ga tsaron Saudiyya, tare da cewa firaministan ƙasar ya bayar da umarnin gudanar da bincike domin gano waɗanda ke da hannu a hare-haren, kamar yadda wata sanarwa daga rundunar sojin ƙasar ta bayyana.

Tun bayan fara yaƙin Amurka da Iraƙi, Riyadh ta ƙara amfani da wannan bututun mai, wanda ya haɗa Abqaiq, kusa da Tekun Fasha, da tashar jiragen ruwa ta Yanbu da ke Bahar Maliya, domin kauce wa rufe mashigar ruwan Hormuz da Iraƙi ta yi.