| Hausa
WASANNI
1 minti karatu
Hatsarin mota ya rutsa da Anthony Joshua a jihar Ogun ta Nijeriya
Gwarzon ɗanwasan boksin, Anthony Joshua ya samu hatsarin mota a jihar Ogun ta Nijeriya, inda rahotanni suka ce har mutum biyu sun rasa ransu a motar da yake.
Hatsarin mota ya rutsa da Anthony Joshua a jihar Ogun ta Nijeriya
Shekarun Anthony Joshua 36 kuma a kwanakin bayan ne ya doke Jake Paul / Reuters
29 Disamba 2025

Rahotanni daga Nijeriya na cewa hatsarin mota ya rutsa da gwarzon ɗan damben boksin na Burtaniya ɗan asalin Nijeriya, Anthony Joshua.

Hatsarin wanda hukumomi suka tabbatar ya afku ne a jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Nijeriya, kuma ya bar Joshua da raunuka ba masu tsanani ba.

Mai shekaru 36, Joshua yana tafiya ne cikin mota ƙirar Lexus jeep kan hanyar Lagos zuwa Ibadan, inda motar ta yi karo da wata babbar mota da aka ajiye a gefen hanya.

Joshua yana da dangi a garin Sagamu na jihar Ogun ya tabbatarwa majoyoyin ‘yansanda cewa yana cikin ƙoshin lafiya, duk da rahotanni sun ce mutane biyu sun halaka sakamakon hatsarin.

A halin yanzu wasu hotuna na ta yawo a kafofin yaɗa labarai wanda ke iƙirarin nuna abin da ya faru bayan hatsarin, inda aka ga mota da gilashi a fashe.

Jaridar Punch ta Nijeriya ta nuna wani hoton Anthony Joshua yana zaune a kujerar bayan motar da ta lalace daga gabanta.

Ɗanwasan dai ya kai ziyara Nijeriya ne domin hutun ƙarshen shekara, ‘yan kwanaki bayan ya yi nasara kan Jake Paul a birnin Miami na Amurka ranar 19 ga Disamba.

Rumbun Labarai
Kwana 500 babu aski: Yadda sumar Frank Ilett ta zama shaidar matsalar Man United
Toni Kroos ya soki gasar ƙwallo ta Saudiyya game da raina tasirin Ronaldo
Victor Osimhen ya ci ƙwallo ta 200 a rayuwarsa ta wasa
Atletico Madrid ta ce ta cim ma yarjejeniya da Atalanta kan ɗanwasan gaban Nijeriya Ademola Lookman
Real Madrid za ta sake karawa da Benfica a wasan cike gurbi na Gasar Zakarun Turai
Mourinho ya bai wa Kocin Real Madrid haƙuri bayan Benfica ta doke Madrid a Gasar Zakarun Turai
CAF ta dakatar da kocin Senegal da Achraf Hakimi
Cole Palmer na son komawa Man United, Liverpool ba za ta rabu da kyaftin dinta, Virgil van Dijk ba
'Yanwasan Senegal sun samu kyautar kuɗi da fuloti saboda lashe Kofin AFCON
Dubban mutane sun halarci bikin karrama Zakarun Kofin AFCON a Senegal
Real Madrid ta sallami Xabi Alonso, ta nada Alvaro Arbeloa sabon koci
Hukumar CAF ta yi tir da rashin ɗa'a a zagayen kwata-fainal na AFCON 2025
Ɗan wasan Ghana Semenyo ya koma Man City daga Bournemouth kan dala miliyan 87
Yadda ƙarin kuɗaɗen tallafi ke taimaka wa mata ‘yanwasan ƙwallon ƙafa da ke fama da nakasa a Kenya
Wane ne Liam Rosenior, sabon kocin Chelsea?
Manchester United ta kori kocinta Ruben Amorim bayan ya soki shugabancin kungiyar
An sallami Anthony Joshua daga asibiti
Abubuwa 5 game da mai jiran Man United ta ci wasa 5 a jere, wanda ya kwana 452 ba aski
Yadda Tanzania ta tsallaka gaba da maki biyu kacal a gasar AFCON 2025
AFCON 2025: Za a fara wasannin ƙarshe na matakin rukuni don tantance ƙasashe 16 masu tsallakawa gaba