| hausa
NIJERIYA
3 minti karatu
An kashe fiye da mutane 20 a sababbin hare-hare a jihar Plateau
An kashe fiye da mutane 20 a hare-hare a jihar Flitao da ke a arewa maso tsakiyar Najeriya a wannan mako, kamar yadda jam'ian ƙarama hukumar Mangu da majiyoyin agaji suka bayyana a ranar Laraba.
An kashe fiye da mutane 20 a sababbin hare-hare a jihar Plateau
Herder-farmer attacks in Nigeria have increased in recent times as pastureland shrinks due to climate change effects.
11 Yuni 2025

Hare-hare a jihar Filato da ke arewa maso tsakiyar Najeriya sun yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 20 a wannan makon, kamar yadda hukumomin yanki da majiyoyin agaji suka bayyana a ranar Laraba.

Hare-haren uku da aka kai a ƙaramar hukumar Mangu sun biyo bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya da aka fara tun lokacin da mutane ke haƙar ma’adanai a yankin da ke da arzikin tin, kamar yadda shugaban ƙaramar hukumar, Emmanuel Bala ya bayyana wa kamfanin dillancin labarai na AFP.

An jima ana samun rikici tsakanin makiyaya da manoma a jihar Filato, kan samun damar amfani da filaye da albarkatun ƙasa.

Hare-hare a yankin galibi suna da alaƙa da ƙabilanci da addini, waɗanda ke haifar da ramuwar gayya tsakanin ɓangarori daban-daban.

Ramuwar Gayya

“A wani lokaci a baya, mutanen yankin suna haƙar ma’adanai, sai aka kai musu hari” da adduna, duk da cewa babu wanda ya mutu a lokacin, in ji Bala ga AFP.

Bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya, an samu hare-hare guda uku a ranar Litinin da Talata, wanɗanda suka yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 20, in ji Bala.

A daren Talata, mutane takwas sun mutu a ƙauyen Chinchin sakamakon wani hari da ake zargin Fulani ne suka kai, in ji Bala.

Wannan harin ya biyo bayan wani hari da aka kai a wajen garin Langai a ranar Litinin, inda mutane biyar suka mutu.

Makiyaya Fulani a yankin suma sun fuskanci hare-hare da cin zarafi a kwanakin baya, bayan hare-haren da ake zargin wasu daga cikin kabilar su ne suka kai, in ji Bala.

Mummunar gwagwarmaya kan filaye

Haka kuma a ranar Litinin, wasu mahara da ba a san ko su waye ba sun kashe mutane bakwai a yankin Bwe.

Wani jami’in Red Cross ya tabbatar da adadin mutanen da suka mutu a Chinchin kuma ya ce yawan waɗanda suka mutu a cikin sa’o’i 24 zai iya kaiwa 21.

Filayen da manoma da makiyaya ke amfani da su a tsakiyar Najeriya suna fuskantar ƙalubale daga sauyin yanayi da ƙaruwar yawan jama’a, wanɗanda ke haifar da gasa mai tsanani kan taƙaitattun filayen.

Harin ramuwar Gayya

Ƙwace filaye, da rikice-rikicen siyasa da tattalin arziki tsakanin mazauna yankin da waɗanda ake ɗauka a matsayin baƙi, da kuma ƙaruwar masu wa’azin addinai masu tsattsauran ra’ayi, sun ƙara raba kan jama’a a cikin ‘yan shekarun nan.

Idan tashin hankali ya ɓarke, rashin karfin ‘yan sanda na iya haifar da ramuwar gayya, wanda galibi ke faruwa tsakanin al’ummomi daban-daban.

A watan Afrilu kaɗai, hare-hare da aka kai a Filato da jihar Benue da ke maƙwabtaka sun yi sanadin mutuwar fiye da mutane 150.

Rumbun Labarai
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka
Trump ya umarci Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya