Hanyoyin kauce wa kamuwa da kansar baki da ke kashe mutum 700 duk shekara a Nijeriya
DUNIYA
5 MINTI KARATU
Hanyoyin kauce wa kamuwa da kansar baki da ke kashe mutum 700 duk shekara a NijeriyaMa’aikatar Lafiya ta Nijeriya ta tabbatar da cewa a duk shekara sama mutum 700 ke mutuwa sakamakon cutar sankarar baki a kasar.
Cutar sankarar baki wani nau’in ciwon daji ne da ke shafar sassan bakin dan adam kamar lebe da dasashi da hakori da harshe da makogwaro da cikin kumatu / Hoto: WHO Africa / Others

Daga Shamsiyya Hamza Ibrahim

Kwararru a fannin kiwon lafiya a Nijeriya sun bayyana damuwa kan yadda ake samun karuwar masu kamuwa da cutar kansar baki a kasar.

Masana harkar lafiyar sun alakanta karuwar cutar da rashin daukar kula da baki da muhimmanci da mafi yawan mutane ke yi musamman a yankunan karkara.

Hakan na zuwa ne a yayin da Ma'aikatar Lafiya ta kasar ta ce cutar kansar baki na kashe a kalla mutum 746 duk shekara a Nijeriya sakamakon rashin ziyartar cibiyoyin lafiya a kan lokaci.

A yayin da yake jawabi a taron horarwa kan hanyoyin kula da baki da Gidauniyar Cleft and facila Deformity CFDF ta gudanar a karshen makon jiya, Ministan Lafiya na Nijeriya Dakta Osagie Ehanire ya ce adadin masu kamuwa da cutar sankarar baki kan kai 1,146 a duk shekara a kasar.

Yadda ake kamuwa da ita

"Cutar sankarar baki wani nau’in ciwon daji ne da ke shafar sassan bakin dan adam kamar lebe da dasashi da hakori da harshe da makogwaro da cikin kumatu da handa da ganda da dai sauransu," a cewar Dakta Muhammad Adam na Babban Asibitin Birnin Kudu da ke jihar Jigawa a Nijeriya.

A hirarsa da TRT Afrika, Dakta Adam ya ce cutar ta fi shafar maza da kuma wadanda shekarunsu suka haura 50, sannan ta fi yawa a kasahen fararen fata.

Likitan ya bayyana wadansu abubuwa da ka iya jawo cutar kamar “sinadarin nicotin da ke cikin taba sigari ko tabar hayaki ta shisha ko kuma tabar taunawa, da shan giya da kayan maye da kuma kwayar cutar virus mai suna HPV (human papilloma virus).

"Kazalika ana gadonta daga iyaye da kakanni, da yawan shiga matsananciyar rana a kasashen fararen fata, da rashin garkuwar jiki mai karfi, duk suna cikin hanyoyin da ake kamuwa da cutar,” in ji likitan.

Dakta Razina Abbas Kwararriyar likitar kula da baki ce a cibiyar sashin kula da baki ta Jami’ar Ahmadu Bello ABU da ke Zaria, ta gaya wa TRT Afrika cewa rashin wanke baki yadda ya kamata bayan an ci abinci ma ka iya jawo cutar.

"Saboda kwayar cutar bakteriya na iya zama a cikin bakin kuma ta haifar da matsalar cutar kansa."

"Kuma ire- iren abincin da ake ci ba tare da wanke baki da sinadaren da ya kamata ba ya sa ake dada samun karuwar cutar a Nijeriya,'' a cewar Dakta Razina.

Shi ma Dakta Adam ya jaddada cewa rashin kula baki da mafi yawan mutane ke yi musamman a yankunan karkara na ta'azzara lamarin.

''Baki na daga cikin sassan jiki masu muhimmanci kuma idan ba a kula da shi ba za a iya fuskantar matsala domin yawancin cututtuka na shiga jikin dan adam ne ta baki.

Hanyoyin magance ko takaita cutar

Kwararru sun ce idan an gane ta da wuri kafin ta yadu ana warkewa.

Amma idan ta yadu yawanci nakasa mutum take har zuwa mutuwa, a cewarsu.

Akwai hanyoyin da za ka iya bi wajen kare kanka daga kamuwa da cutar in ji Dakta Muhammad Adam.

  • Daina amfani da sinadaran nicotin da ke kunshe a taba sigari da sauransu da aka ambata a baya

  • Daina shan giya da kayan maye

  • Yin rigakafin cutar HPV

  • Yawan cin kayan lambu kamar manyan lemon tsami da karas don za su taimaka wajen gyara baki

  • Wanke baki da sinadarin Floride zai taimaka wajen kashe kwayoyin cuta da ke iya cutar da baki

  • Zuwa asibiti don duba sassan cikin baki musamman bangaren likitocin baki da hakori, duk bayan wata shida ko kuma ko da sau daya a shekara

  • Yawan wayar da kan al’umma.

An ware kowane watan Afrilu na duk shekara a matsayin watan wayar da kan al’umma kan cutar sankarar baki.

An yi hakan ne don likitoci da kwararru a fannin kula da baki su dinga haduwa suna fadakar da mutane illar da ke tattare da cutar da hanyoyin magance ta, da kuma inda aka kwana game da yaki da ake yi da ita.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Damuwar 'yan Republican na ƙaruwa gabanin zaɓukan rabin wa'adi saboda tasirin yaƙin Iran
Chadi za ta tura sojoji 750 domin yaƙar 'yandaban Haiti
Trump: Amurka na duba yiwuwar 'kammala' hare-haren soji kan Iran
NATO na fuskantar ‘mummunar makoma’ idan ƙasashenta suka ƙi taimaka wa Amurka a yaƙin Iran - Trump
Trump ya ce bai shirya yin yarjejeniya ba domin kawo ƙarshen yaƙin Iran
Tsarin kiwon lafiya a Gabas ta Tsakiya na fuskantar barazana yayin da rikici ke ƙara muni: WHO
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya
Mashigar Hormuz: Hanyar ruwan da za ta iya girgiza tattalin arzikin duniya
Dalilai huɗu da suka sa matasan Afirka suka fi lafiyar ƙwaƙwalwa a duniya
Musulmai a Turkiyya, Oman, Singapore, da Australia za su fara azumin Ramadan a ranar Alhamis
'Babu wani takamaiman abin da aka cim ma' a ganawar Trump da Netanyahu a kan Iran
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba
Trevor Noah: Trump ya yi barazanar maka mai gabatarwa a Gasar Grammy a Kotu
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran