AFIRKA
2 MINTI KARATU
Ba na neman mukami a gwamnatin Tinubu - Elrufai
Elrufai ya ce idan ya sauka daga mulki a karshen watan Mayu zai mayar da hankali kan fannin 'yan kasuwa masu zaman kansu.
Ba na neman mukami a gwamnatin Tinubu - Elrufai
Elrufai ya ce zai mayar da hankali a fannin 'yan kasuwa masu zaman kansu. Hoto/@GovKaduna
7 Mayu 2023

Gwamnan Jihar Kaduna da ke arewacin Nijeriya, Nasir Elrufai, ya musanta rade-radin da ake yi cewa zai zama shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa a gwamnatin zababben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana haka ne a Gombe ranar Asabar yayin da ya ziyarci Jihar don kaddamar da wasu ayyuka da Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya ya gudanar.

Elrufai ya ce idan ya sauka daga mulki a karshen watan Mayu zai mayar da hankali kan fannin 'yan kasuwa masu zaman kansu.

"Ban tattauna da zababben shugaban kasa (a kan wannan batu ba) kuma ba na son jita-jita. Na karanta a jaridu cewa za a ba ni wasu mukamai. Ina son kasata da kuma ci gabanta. Amma ba sai na yi aiki a cikin gwamnati ba.

“Akwai hanya fiye da daya da za ka taimaka wajen cigaban kasar nan kuma ba zan taba daina aiki don cigaban Nijeriya ba. Zan kasance a bangaren 'yan kasuwa masu zaman kansu, ba shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa ba."

Gwamna Elrufai ya ce zai yi hutu bayan ya sauka daga mulki sannan ya rika ba da shawara ga masu mulki idan suka bukaci hakan daga gare shi.

Gwamnan na Kaduna, wanda a baya ya rike mukamai ciki har da ministan babban birnin tarayya Abuja, yana cikin mutanen da suka taka muhimmiyar rawa wajen nasarar jam'iyyar APC da kuma goyon bayan dan takararta na shugaban kasa, Bola Tinubu.

Hakan ne ya sa ake ta yada jita-jita a kan yiwuwar nada shi a matsayin shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar