AFIRKA
5 MINTI KARATU
Abu uku da Elrufai ya fada a hirarsa ta 'bankwana'
Gwamna Elrufai mai barin gado ya tabbatar da cewa gwamnatinsa ta yi aiki a duka gundumomi da ke jihar.
Abu uku da Elrufai ya fada a hirarsa ta 'bankwana'
A ranar 29 ga watan Mayu Elrufai zai mika mulki ga zababben gwamnan Malam Uba Sani. Hoto/Nasir El Rufai
22 Mayu 2023

Gwamna Malam Nasiru Elrufai ya bayyana irin nasarorin da ya samu a matsayinsa na gwamnan Jihar Kaduna da ke arewacin Nijeriya.

A wata tattaunawa ta bankwana da gwamnan jihar ya yi da gidan talabijin din jihar wato KSMC, gwamnan ya yi godiya ga jama’ar Jihar Kaduna kan damar da suka ba shi tare kuma da fadin yadda tafiyar ta kasance.

A ranar 29 ga watan Mayu ne zai mika mulkin jihar ga zababben gwamnan Malam Uba Sani. Ga wasu daga cikin muhimman abubuwan da gwamnan mai barin gado ya bayyana a yayin tattaunawar:

'Mun yi tsari a Kaduna har zuwa shekarar 2050'

Gwamna Elrufai ya bayyana cewa a tsawon mulkinsa, sun yi tsarin ayyuka da za a ci gaba da tafiyarwa har zuwa shekarar 2050.

“Duka tsare-tsaren sunan nan, wanda kawai za ka yi ka dauka ka bi abin da aka tsara, idan akwai wani gyara da za a yi sai a gyara,” in ji Gwamna Elrufai.

“Wannan tsarin ba wai na hanyoyi ba ne kadai domin mutane sun fi ganin hanyoyi, amma tsari ne wanda baya ga hanyoyi akwai kasuwanni akwai wuraren ayyuka wato masana’antu da ofisoshi da wuraren sayen kayayyaki.

Duka an saka su a wannan tsari daga 2018 har zuwa 2050, kuma duk wanda yake so ya bi wannan tsarin zai ga ci gaban Jihar Kaduna.

Ma’aikata daya da ke samar da akalla biliyan 12 a shekara

A cikin hirar da Gwamnan Jihar Kaduna ya yi, ya bayyana cewa ma’aikatar kula da filaye da safiyo wadda suka sauya ta koma KADGIS a halin yanzu tana samar wa jihar kudaden shiga masu dumbin yawa.

Ya bayyana cewa sakamakon garambawul da suka yi wa ma’aikatar da kuma irin sabbin tsare-tsare da suka kawo, akwai akalla jihohin Nijeriya bakwai da suke son daukar tsarin KADGIS.

Ba na neman mukami a gwamnatin Tinubu - Elrufai

“A shekara daya idan ba mu tara kudi daga KADGIS ba, mu tara biliyan 12, wato kowane wata muna samun kusan naira biliyan daya daga KADGIS kawai,” in ji gwamnan.

Ya bayyana cewa a gwamnatocin baya kudin da ma’aikatar kula da filaye da safiyo ke samarwa a wata ba ya wuce miliyan 100.

Ya kuma bayyana cewa a baya idan mutum yana son sahihan takardun fili ko kadararsa, sai ya dauki fiye da shekara uku yana jira, amma a halin yanzu cikin watanni ko kwanaki mutum zai iya samu.

'Mun yi aiki a duka gundumomin Kaduna'

Gwamnan Jihar Kaduna ya yi karin bayani kan korafe-korafen da ake yi kan cewa a tsawon mulkinsa na shekara takwas, a cikin kwaryar Jihar Kaduna kawai ya yi aiki.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi aiki a duka gundumomi da ke cikin jihar.

“Babu gunduma a Jihar Kaduna da ba mu gyara asibiti ba, babu gunduma da ba mu gyara makarantu ba, babu karamar hukumar da ba mu bayar da kwangilar a yi hanyoyi na kilomita goma ba,” in ji Elrufai.

Ya bayyana cewa kan batun hanyoyin akwai wuraren da ba a samu an yi su ba sakamakon matsalolin tsaro inda ya bayar da misali da Zangon Kataf.

“A kauyuka, mun yi titi kusan kilomita 172 domin duk inda muka ga ana da amfanin gona babu hanyar da za a kawo shi kasuwa, za mu je mu yi hanya,” in ji gwamnan

A ranar Litinin 29 ga watan Mayu ne Gwamna Nasir zai sauka daga mulki bayan shafe shekara takwas, inda zai mika wa Malam Uba Sani na jam'iyyarsa ta APC wanda ya lashe zaben watan Maris din 2023.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci
Rundunar RSF ta amsa aikata 'take haƙƙi' a Al Fasher na Sudan
Kenya ta tabbatar da mutuwar mutum 11 'yan yawon bude ido a hatsarin jirgin da aka yi a kasar