| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Adadin wadanda suka mutu a harin masallaci a Malumfashin Jihar Katsina ya kai 50
Gwamnati ta ce rundunonin tsaro sun shiga yankin don dawo da lafiya.
Adadin wadanda suka mutu a harin masallaci a Malumfashin Jihar Katsina ya kai 50
Adadin wadanda suka mutu a harin masallaci a Malumfashin Jihar Katsina ya kai 50 / Reuters
20 Agusta 2025

Adadin mutanen da suka mutu a wani hari da ‘yan bindiga suka kai wani masallaci a garin Malumfashi da ke arewa maso yammacin Nijeriya a ranar Talata, ya kai 50, sannan maharan sun kuma sace fiye da mutum 60, kamar yadda jami’an yankin da mazauna garin suka fada a ranar Laraba.

Tun da fari a ranar Larabar wani mazaunin yankin da kuma wani dan majalisar jiha ya ce adadin wadanda suka mutun ya kai 30 daga 13 da aka fara bayarwa.

‘Yan ta’addan sun kai hari ne kan masallacin a garin Unguwar Mantau a yayin da suke Sallar Asuba, inda masu bibiyar rikice-rikice suka bayyana cewa mutum 13 ne suka fara mutuwa.

“An kashe mutane tara a wurin nan take, sannan wasu da dama sun mutu a yinin ranar. Adadin yanzu ya kai 32,” in ji wani mazaunin yankin mai suna Nura Musa a ranar Laraba.

Wani ɗan siyasa na yankin, Aminu Ibrahim, ya shaida wa Majalisar Dokokin Jihar Katsina a ranar Talata cewa mutane 30 aka kashe.

Wani bayani daga Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Gida na Jihar Katsina, Dr Nasir Muazu, ya ce harin na ramuwa ne saboda nasarar da al’ummar Unguwar Mantau suka samu a kwanaki biyu da suka gabata, inda suka yi wa ‘yan ta’adda kwanton bauna suka kashe da dama daga cikinsu.

A halin yanzu, gwamnati ta ce an tura jami’an tsaro zuwa yankin domin dawo da zaman lafiya.

Matsalar ‘yan fashi a yankunan arewa maso yamma da arewa ta tsakiya na Nijeriya tana zama babban ƙalubale ga tsaro.

Wadannan kungiyoyi sun shahara wajen aikata ta’addanci, kai hare-hare kan kauyuka, sace mutane don neman kudin fansa da kuma kwashe dukiyoyi.

Shugaba Bola Tinubu yana daukar matsaya mai tsauri kan ‘yan fashi da ‘yan ta’adda a Nijeriya domin magance wannan matsala, a cewar jami’an gwamnatinsa.

Rumbun Labarai
Shugaban Nijeriya Tinubu na neman sake aro dala biliyan 6 daga UAE da Birtaniya
Zanga-zanga ta ɓarke a Afirka Ta Kudu kan naɗin Sarkin 'yan ƙabilar Igbo
'Yanbindiga sun kashe mahalarta ɗaurin aure 13, sun yi garkuwa da wasu a Kaduna
Ɗumbin magoya bayan Kwankwasiyya sun halarci taron komawar Kwankwaso Jam'iyyar ADC
Gwamnatin Jihar Filaton Nijeriya ta saka dokar hana fita ta sa'o'i 48 a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa
Sojojin Nijeriya sun daƙile harin ISWAP, sun kashe ‘yanta’adda 38 a Borno
APC ta kammala babban taronta na ƙasa, Nentawe Yilwatda zai ci gaba da zama shugaban jam'iyyar
Nijeriya ta ƙaddamar da shirin riga-kafin HIV, na allurar Lenacapavir
NCC za ta toshe layukan waya masu alaka da damfara a Nijeriya
Nijeriya ta sassauta dokokin kuɗaden waje, kamfanonin man ƙetare za su iya fitar da duk kuɗaɗensu
'Yanta'addan Lakurawa sun kashe sojoji 11 da ɗansanda a harin kwanton-ɓauna a Jihar Kebbin Nijeriya
Sojojin ruwan Nijeriya sun kama masu tserewa Turai a ɓoye ta jirgin ruwa a Legas
NEMA ta karɓi 'yan Nijeriya 708 da suka maƙale a Jamhuriyar Nijar
Zarge-zargen da hukumar ICPC ke yi wa Nasir El-Rufai
Jami’ar Bayero ta Kano ta kori ɗalibai 171 bisa laifin gabatar da takardun bogi
Kotu ta yi wa tsohon babban akantan Nijeriya ɗaurin shekara 72 a gidan yari kan damfarar N868m
Taron gwamnoni a Legas ne ya hana ni zuwa Bikin Hawan Nasarawa – Gwamnan Kano
Tashin farashin mai a Nijeriya ya yi ƙamari yayin da yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran ya ƙi ƙarewa
Amurka ta tura jirage marasa matuƙa Nijeriya don tattara bayanan sirri kan 'yanta'adda
Sarki Charles ya amince da ‘mummunan’ mulkin mallakar da Birtaniya ta yi wa Nijeriya