| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Kasashe 6 a Afirka na asarar $2.3bn sakamakon kamun kifi da ake yi ba bisa ka'ida ba
Rahoton Amnesty ya ce Gambiya da Mauritaniya da Guinea Bissau da Guinea da kuma Sierra Leone na asarar akalla dala biliyan 2.3 a duk shekarar saboda kamun kifi ba bisa ka’ida ba.
Kasashe 6 a Afirka na asarar $2.3bn sakamakon kamun kifi da ake yi ba bisa ka'ida ba
Kasashe shida a Afirka na asarar akalla dala biliyan 2.3 a duk shekara saboda kamun kifi ba bisa ka'ida ba. Hoto: Getty
2 Yuni 2023

Daga Brian Okoth

Wani rahoto da Kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International ta fitar kan yadda ake kamun kifi ya bayyana cewa kasashe shida suna asarar akalla dala biliyan 2.3 duk shekara sakamakon kamun kifi ba bisa ka'ida ba.

Kasar Gambia da Mauritania da Senegal da Guinea Bissau da Guinea da kuma Sierra Leone na asarar kudaden a duk shekara, a cewar rahoton.

A wani bincike da kungiyar ta gudanar a Gambia daga watan Yunin 2021 zuwa Afrilun 2022 ta gano cewa wasu kamfanoni na kasashen waje da ke amfani da na'urori na zamani suna yin kamun kifi ba bisa ka'ida ba a cikin ruwan kasar.

"Dole ne gwamnatin Gambia da wasu kungiyoyin kasashen waje da ke aiki a yankunan da abin ya shafa su tabbatar cewa jiragen ruwa na kasashen waje da masana'antun kifi suna mutunta dokokin kamun kifi na kasar da kuma na kasa da kasa," in ji Amnesty.

“Yana da muhimmanci al'ummomin yankin su ci gaba da samun damar kama kifi ta amfani da hanyoyin da za su dore.”

Kauyen Sanyang da ke gabar teku a kudu maso yammacin Gambiya, shi ya fi fama da wannan matsala ta kamun kifi ba bisa ka'ida ba, inda rahoton ya nuna cewa halin da ake ciki a wajen ya "tsananta".

A 2017 ne aka gina wata masana'antar sarrafa kifi ta kasashen waje a kauyen kuma bayan ta fara aiki a shekarar 2018, al'ummar yankin sun ce ayyukan raya tattalin arzikinsu sun yi kasa sosai.

Masu gidajen cin abinci da wuraren shakatawa da ke gabar tekun sun ce sun yi asarar kwastamominsu saboda warin da ke fitowa daga masana'antar.

Kazalika masunta a kasar sun ce manyan jiragen ruwa da kamfanonin kasashen waje ke aiki da su, sun matukar taimaka wajen rage yawan kifayen ruwan.

Amnesty ta ce "dole" hukumomin Gambia da kasashen duniya su dauki matakia yanzu don kare hakkin al'ummomin da ke kamun kifi da kuma kiyaye muhalli.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta