AFIRKA
3 minti karatu
Odinga: Ruto ya ayyana makokin kwana bakwai a Kenya don jimamin mutuwar tsohon firaministan ƙasar
Shugabannin ƙasashen Afirka da na duniya suna ta aikewa da saƙonnin ta'aziyya ga ƙasar Kenya kan rasuwar Odinga.
Odinga: Ruto ya ayyana makokin kwana bakwai a Kenya don jimamin mutuwar tsohon firaministan ƙasar
An yabawa Odinga kan ƙoƙarinsa a fannin haɗin kan Afirka
15 Oktoba 2025

Shugaban kasar Kenya, William Ruto ya ayyana kwanaki bakwai na zaman makoki na kasa baki daya bayan rasuwar jagoran adawa kuma tsohon Firaminista Raila Odinga, tare da sanar da cewa za a yi masa jana'izar ban-girma ta ƙasa.

An ruwaito cewa Odinga mai shekaru 80, ya yanke jiki ya fadi yayin da yake tattaki da safe a cikin wani wurin magani na Ayurvedic da ke Koothattukulam a India. An garzaya da shi zuwa wani asibiti mai zaman kansa, inda aka tabbatar da rasuwarsa da karfe 9:52 na safe agogon yankin.

A cikin wani jawabi na kasa da ya yi a ranar Laraba, Shugaba Ruto ya yi wa Odinga jinjina, yana bayyana shi a matsayin “jagora mara tsoro” da kuma dattijo wanda tasirinsa ya tsara yanayin siyasar Kenya tsawon shekaru da dama.

“A cikin girmamawa ga gudunmawar da mai girma Raila Odinga ya bayar ga kasarmu, na ayyana kwanaki bakwai na zaman makoki na kasa, inda tutar kasa za ta kasance a ƙasa-ƙasa a fadin Jamhuriyar Kenya da dukkan ofisoshinmu na jakadanci a kasashen waje,” in ji Ruto.

Sakon ta'aziyya

Shugabannin ƙasashen Afirka da na duniya suna ta aikewa da saƙonnin ta'aziyya ga ƙasar Kenya kan rasuwar Odinga.

Shugaban Hukumar Tarayyar Afirka (AUC) ya bayyana Odinga a matsayin “babban mutum a siyasar Kenya.”

“Gudunmawar Odinga ta wuce iyakokin kasa. A matsayinsa na Wakilin Musamman na Tarayyar Afirka kan Cigaban Ababen More Rayuwa a Afirka, ya yi aiki tukuru wajen bunkasa shirin hadin kan nahiyar da kuma inganta hanyoyin sadarwa, wanda ya taimaka wajen kafa harsashin Yarjejeniyar Ciniki ta Nahiyar Afirka (AfCFTA) da kuma sauye-sauyen tattalin arziki da zamantakewa,” in ji AUC a cikin girmamawar da ta yi masa.

Hukumar ta kara da cewa za ta “ci gaba da tuna da sadaukarwar Odinga na tsawon shekaru wajen tabbatar da adalci, bambancin ra'ayi, da sauye-sauyen dimokuradiyya,” wanda ya bar “tabo mai zurfi ba kawai a Kenya ba, har ma a fadin nahiyar Afirka.”

Haka zalika, Sakatare Janar na Kungiyar Raya Yankin Gabas (IGAD), Workneh Gebeyehu, ya bayyana ta'aziyyarsa, yana yabawa da sadaukarwar Odinga ga dimokuradiyya da manufofin haɗin-kan Afirka.

“A matsayinsa na mai kishin Afirka, ya sadaukar da rayuwarsa wajen neman dimokuradiyya, adalci, da hadin kai.

“Gwaggwarmayarsa ta tsawon rayuwa don 'yanci da daidaito ta zamo abin koyi ga al'ummomi a fadin Kenya da ma duniya baki daya, tana tunatar da mu cewa jagoranci ba wai game da iko ba ne, amma game da hidima da sadaukarwa,” in ji Gebeyehu.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya