| hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
Putin ya gaya wa shugabannin Afirka a shirye yake ya yi sulhu da Ukraine
Tawagar shugabannin Afirka ta gana da Shugaba Putin ranar Asabar bayan ta gana da takwaransa na Ukraine Volodymyr Zelensky ranar Juma'a.
Putin ya gaya wa shugabannin Afirka a shirye yake ya yi sulhu da Ukraine
Shugaba Ramaphosa ya ce yakin Rasha da Ukraine yana mummunan tasiri kan kasashen Afirka./Hoto:Getty
17 Yuni 2023

Shugabannin kasashen Afirka da ke neman yin sulhu tsakanin Rasha da Ukraine ta shaida wa Shugaba Vladimir Putin cewa lokaci ya yi da za a kawo karshen yakin da kasashen ke yi.

Sun bayyana hakan ne ranar Asabar a yayin ziyarar da suka kai kasar ta Rasha suna masu cewa yakin yana yin illa ga Afirka da ma daukacin duniya.

Tawagar ta kunshi shugabannin kasashen Senegal, Macky Sall; Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa; Zambia, Hakainde Hichilema; Comoros, Azali Assoumani, wanda shi ne shugaban Tarayyar Afirka; da kuma firaiministan Masar.

"Mun zo nan ne domin mu mika sako karara cewa ya kamata a kawo karshen wannan yakin... dole ne a yi sulhu ta hanyar diflomasiyya," in ji Shugaba Cyril Ramaphosa, a taron manema labaran da suka gabatar a St Petersburg.

A nasa bangaren, Shugaba Putin ya yi "maraba da sigar Afirka ta adalci" a wannan rikici yana mai cewa "kofarmu a bude take mu yi tattaunawa mai ma'ana tare da dukkan wadanda suke son wanzar da zaman lafiya bisa adalci da mutunta juna."

Tun da fari tawagar shugabannin Afirka ta gana da Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ranar Juma'a domin yin sulhu tsakaninsa sa takwaransa na Rasha.

Shugaba Zelensky ya gayyaci shugabannin Afirka su halarci "taron kasashen duniya na samar da zaman lafiya" inda zai gabatar da "tsarin zaman lafiya."

Shugabannin Afirka su ne na baya bayan nan da ke yunkurin yin sulhu a yakin da aka soma a watan Fabrairun bara wanda ya yi sanadin mutuwar dubban mutane.

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda
Rumbun Labarai
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta