| hausa
AFIRKA
2 MINTI KARATU
Kwale-kwale ya kife da dalibai a Nijeriya
Amma har yanzu ba a ga dalibai uku ba kuma ana ci gaba da nemansu, a cewar NTA.
Kwale-kwale ya kife da dalibai a Nijeriya
Mako jiya fiye da mutum 150 sun mutu a Nijeriya sakamakon hatsarin kwale-kwale./Hoto:OTHER
25 Yuni 2023

Wani kwale-kwale dauke da dalibai ya kife a kogin Calabar-Oron a jihar Cross River da ke kudu maso kudancin kasar.

Gidan talbijin na Nigeria Television Authority, NTA, ya bayyana cewa kwale-kwalen yana dauke da daliban da ke karatun aikin likita 14 yayin da ya kife.

A sakon da NTA ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Asabar da tsakar dare ya ce daliban, karkashin kungiyarsu ta NIMSA , sun je Calabar ne a wani bangare na bikin da suke yin shekara-shekara amma sai suka yanke shawarar shiga kwale-kwale don kashe kwarkwatar idanunsu a wurin shakatawa na Calabar Marina Resort.

Sai dai "abin takaici shi ne kwale-kwalen ya kife" amma dalibai 14 sun yi sa'a bayan da jirgin rundunar sojin ruwa na kasar, wanda ke kusa da su a lokacin, ya yi gaggawar ceto su.

Amma har yanzu ba a ga dalibai uku ba kuma ana ci gaba da nemansu, a cewar NTA.

Ana fuskantar hatsarin kwale-kwale lokaci zuwa lokaci a Nijeriya sakamakon sanya mutane fiye da kima da kuma rashin ingancinsu.

A farkon watan nan, wani kwale-kwale da ya kwaso fiye da mutum 300 ya yi hatsari a jihar Kwara da ke arewacin kasar lamarin da ya yi sanadin mutuwar fiye da mutum 150.

Hukumomi sun sha cewa suna daukar matakan dakile wannan matsala amma lamarin ya ki ci ya ki cinyewa.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan