| Hausa
DUNIYA
2 MINTI KARATU
Hannayen-jarin kamfanonin Faransa sun fadi bayan juyin mulki a Gabon
Hannayen-jarin kamfanonin Maurel & Prom, Eramet, da reshen TotalEnergies na kasar Gabon sun fadi da kashi 15 zuwa 20, a cewar jaridar Les Echos da ake wallafawa a kowace rana a Faransa.
Hannayen-jarin kamfanonin Faransa sun fadi bayan juyin mulki a Gabon
Faransa ta ce tana sanya ido sosai a kan halin da ake ciki a Gabon. / Hoto: Reuters / Reuters
30 Agusta 2023

Hannayen-jarin kamfanonin Faransa uku sun fadi a kasuwar hada-hadar hannun-jari ta Paris ranar Laraba bayan sojoji sun sanar da kifar da gwamnati a Gabon, inda suke gudanar da harkokinsu.

Hannayen-jarin kamfanonin Maurel & Prom, Eramet, da reshen TotalEnergies na kasar Gabon sun fadi da kashi 15 zuwa 20, a cewar jaridar Les Echos da ake wallafawa a kowace rana a Faransa.

Tun da farko kamfanin hakar ma'adinai na Eramet ya sanar cewa ya dakatar da ayyukansa da kuma sufurin jiragen kasa a Gabon.

Labari mai alaka: Ali Bongo Ondimba ya sake yin nasara a zaben shugaban kasar Gabon

Wasu manyan sojojin Gabon sun bayyana a gian talabijin da sanyin safiyar Laraba inda suka yi ikirarin kifar da gwamnatin Shugaba Ali Bongo.

Sanarwar tasu na zuwa ne jim kadan bayan hukumar zaben kasar ta ayyana Shugaba Bongo a matsayin wanda ya lashe zaben karo na uku indaya samu kashi 64.27 na kuri'un da aka kada.

MAJIYA:AA
Rumbun Labarai
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba
Trevor Noah: Trump ya yi barazanar maka mai gabatarwa a Gasar Grammy a Kotu
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara
Sanatocin Republican 5 sun bi sahun 'yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela