| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Sahel Alliance: Nijar, Burkina Faso da Mali sun kulla kawance
Kasashen sun kafa kungiyar kawance ta Alliance of Sahel States a yayin da dukkansu suke rigima da ECOWAS sakamakon juyin mulkin da aka yi a Nijar a watan Yuli.
Sahel Alliance: Nijar, Burkina Faso da Mali sun kulla kawance
Niger, Burkina Faso da Mali sun ce kawancen zai taimaka wajen samar da zaman lafiya a yankin Sahel. Hoto: Fadar shugaban kasar Nijar/X
16 Satumba 2023

Shugabannin kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar kulla kawancen tsaro da tattalin arziki a tsakaninsu.

Sun kulla yarjejeniyar ce ranar Asabar a Bamako babban birnin Mali.

"A yau, ni da shugabannin kasashen Burkina Faso da Nijar, mun sanya hannu kan yarjejeniyar Liptako-Gourma da ta kafa Kawancen Kasashen Sahel, wato Alliance of Sahel States (AES), wanda zai tattaro bayanai kan sha’anin tsaro da taimaka wa dukkan al’ummominmu", in ji shugaban kasar Mali, Assimi Goita, a sakon da ya wallafa a shafinsa na X, wanda a baya ake kira Twitter.

Yankin Liptako-Gourma – inda kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar suka yi iyaka da juna – ya dade yana fama da matsalolin hare-haren masu tayar da kayar baya.

Kasashen uku suna fuskantar gagarumin rashin tsaro wanda ya somo daga Mali a 2012 sannan ya watsu zuwa Nijar da Burkina Faso a 2015.

Shugaban mulkin sojin Nijar Abdourahmane Tiani ya bayyana yarjejeniyar a matsayin mai cike da ''tarihi'' yana mai cewa "dukkanmu za mu gina al’ummar yankin Sahel mai cike da zaman lafiya da tsaro da hadin kai.''

Dukkan kasashen uku sun yi fama da juyin mulki tun shekarar 2020, na baya-bayan nan shi ne wanda ya faru a Jamhuriyar Nijar a watan Yulin da ya gabata inda sojoji suka kifar da gwamnatin Mohamed Bazoum.

Kasashen sun kafa kungiyar kawance ta Alliance of Sahel States ce a yayin da dukkansu suke rigima da ECOWAS sakamakon juyin mulkin da aka yi a Nijar.

Labari mai alaka: Mali da Burkina Faso sun tura jiragen yaki Nijar

ECOWAS ta yi barazanar yin amfani da karfin soji domin dawo da Bazoum kan mulki amma kasashen uku sun ce za su mayar da martani.

"Wannan kawancen zai kasance na soji da tattalin arziki tsakanin kasashen uku", a cewar Ministan Tsaron Mali Abdoulaye Diop a yayin taron manema labarai ranar Asabar.

Ya kara da cewa "babban burinmu shi ne yaki da ta'addanci a kasashen uku".

Baya ga fama da kungiyoyin ta'addanci da ke da alaka sa Al Qaeda da Islamic State, Mali tana kuma gwagwarmaya da masu tayar da kayar baya na kungiyoyin makiyaya.

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda
Rumbun Labarai
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan