Ivory Coast: Shugaba Ouattara ya sauke firaminista tare da rushe gwamnati
Za su ci gaba da zama a muƙamansu na ɗan lokaci har sai an naɗa sabon firaminista da ƴan majalisar gwamnati, ya ƙara da cewa.
Shugaban ƙasar Ivory Coast Alassane Ouattara ya cire firaminista tare da rusa majalisar gwamnatin kasar, kamar yadda sakataren fadar shugaban kasa Aboudramane Cisse ya faɗa a ranar Juma'a.
Ba a faɗi dalilin ɗaukar matakin ba.
"Shugaban ƙasa yana miƙa godiyarsa ga Firaminista Patrick Achi da dukkan mambobin gwamnatinsa kan jajircewarsu da hidimar da suka yi wa ƙasar a tsawon shekaru," in ji Cisse.
Za su ci gaba da zama a muƙamansu na ɗan lokaci har sai an naɗa sabon firaminista da ƴan majalisar gwamnati, ya ƙara da cewa.
Ba a saba ganin shugabannin ƙasa suna ɗaukar irin waɗannan tsauraran matakan ba a Ivory Coast, da kuma yi wa gwamnatocinsu garanbawul.
A watan Afrilun bara ne Achi ya miƙa takardarsa ta barin aiki da ta mambobin gwamnatinsa bayan da Ouattara ya sanar da shirye-shiryensa na rage yawan ministocin gwamnatin.
Mako guda bayan nan ne aka sake zaɓar firaministan.
A shekarar 2025 ne za a gudanar da zaɓe a Ivory Coast. Ouattara, wanda aka sake zaɓarsa a shekarar 2022, har yanzu bai bayyana ko zai sake tsayawa takarar ta gaba ba.