| Hausa
DUNIYA
3 MINTI KARATU
An soke ziyarar da Firaiministan Czech zai kai Nijeriya saboda 'ba za a iya daukar dawainiyarsa ba'
Gwamnatin Nijeriya ta soke ziyarar da firaiministan Jamhuriyar Czech Petr Fiala zai kai kasar, tana mai cewa ba za ta iya "daukar dawainiyarsa ba."
An soke ziyarar da Firaiministan Czech zai kai Nijeriya saboda 'ba za a iya daukar dawainiyarsa ba'
Jamhuriyar Czech na cikin kasashen da ke goyon bayan Isra'ila a hare-haren da take ci gaba da kai wa Gaza / Hoto: Reuters / Reuters

Gwamnatin Nijeriya ta soke ziyarar da Firaiministan Jamhuriyar Czech Petr Fiala da tawagarsa ta 'yan kasuwa za su kai kasar jim kadan kafin ya tafi kasar, tana mai cewa ba za ta iya daukar dawainiyar ziyarar ba.

Sai dai kafofin watsa labaran Jamhuriyar Czech sun rawaito cewa matakin nan gwamnatin Nijeriya, wanda ta dauka kwana kafin isar Fiala da tawagarsa ta kasuwanci kasar, na da alaka da goyon bayan da Czech take bai wa Isra'ila.

Gwmnatin Nijeriya ta shaida wa tawagar firaiministan cewa ba za ta iya daukar dawainiyar ziyarar Fiala da tawagarsa ba.

Hakan ne ya sa aka soke ziyarar, a cewar kakakin gwamnatin Jamhuriyar Czech Vaclav Smolka a hirarsa da manema labarai a Nairobi, babban birnin Kenya, inda suka je bayan ziyarar da suka kai Ethiopia, a cewar kafar watsa labarai ta Irozhlas.

Ziyarar kwana biyu

An tsara cewa firaiministan da tawagarsa za su isa Nijeriya ranar Talata domin yin ziyarar aiki ta kwana biyu.

Sai dai kafar watsa labarai ta Irozhlas ta ambato wasu majiyoyin diflomasiyya suna cewa matakin na Nijeriya na da nasaba da matsayin Jamhuriyar Czech na goyon bayan Isra'ila a hare-haren da take ci gaba da kai wa Falasdinawa.

Ta kara da cewa Jamhuriar Czech, tare da Amurka da Isra'ila, na cikin kasashe 14 da suka yi fatali da kudurin Majalisar Dinkin Duniya na tsagaita wuta a Gaza ranar 27 ga watan Oktoba.

Isra'ila ta kashe Falasdinawa sama da dubu doma, ciki har da kananan yara 4,237 da mata 2,719 tun lokacin da ta kaddamar da hare-hare a Gaza ranar 7 ga watan Oktoba, a cewar alkaluman baya-bayan nan na Ma'aikatar Kiwon Lafiya ta kasar.

MAJIYA:AA
Rumbun Labarai
Yadda kujerar Firaministan Birtaniya ke komawa tamkar kujerar aski
Trump ya ce ba za a yi yarjejeniyar nukiliya da Saudiyya ba sai ta amince da gyara alaƙa da Isra'ila
Trump ya tarbi gawawwakin sojojin Amurka da aka kashe a yaƙin Iran
Trump ya amince da yarjejeniyar shirin nukiliya na farar-hula da Saudiyya — Rahoto
Sabon Firaministan Birtaniya Burnham ya yi alƙawarin rage tsadar rayuwa
Netanyahu ya fusata Trump bayan ya caccaki shirin Amurka na sayar wa Turkiyya F-35: Rahoto
Ana fargabar mutuwar 'yan ƙabilar Rohingya fiye da 500 bayan kifewar jiragen ruwa a gaɓar Myanmar
Masu ceton dabbobi na taimaka wa tsuntsaye tsira daga bazara mai zafi
Ƙirkirarriyar Basira, ƙarfin intent da ƙa’idojin aikin jarida
Yawan masu kamuwa da cutar kansa na iya kusan ninkuwa nan da shekarar 2050
Mai tsaron bayan Argentina ya ce alƙalan wasan Gasar Kofin Duniya 'na aiki mai kyau'
An kona gini mai kama da masallaci a Arewacin Ireland  a yayin da ‘yansanda ke gudanar da bincike
An samu rahotannin cin zarafin mata kusan 9,800 a shekarar 2025, fiye da ninki biyu kan na 2024: MDD
Mene ne takunkuman CAATSA kuma ta yaya cire su da Amurka za ta yi zai amfani Turkiyya?
Shugaban Koriya ta Arewa ya je kallon gwajin makami mai linzami mai iya ɗaukar nukiliya
Tafiyar al'ajabin Cape Verde ta ƙare, amma ƙasar Afirkan ta fice daga gasar kofin duniya da suna
TikTok da Youtube sun rufe shafukan yara miliyan 4.7 a Indonesia bayan matakan gwamnati
NATO za ta bayyana biliyoyin daloli a wasu sabbin kwangilolin tsaro a taron Ankara
An ɗaure 'yan Nijeriya sha biyu a Jamus saboda 'zamba ta hanyar soyayya'
Venezuela ta ayyana dokar ta-ɓaci bayan tagwayen girgizar ƙasa, ana fargabar dubbai sun mutu