| Hausa
TATTALIN ARZIKI
2 MINTI KARATU
Saudiyya za ta ƙulla yarjejeniyar dala miliyan 500 da ƙasashen Afirka
Ministan Kuɗi na ƙasar Mohammed Al-Jadaan ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis, yayin wani Taron Tattalin Arziki na Saudiyya da Ƙasashen Afirka da ake gudanarwa a birnin Riyadh.
Saudiyya za ta ƙulla yarjejeniyar dala miliyan 500 da ƙasashen Afirka
“Muna aiki da abokan hulɗarmu don tallafa wa Ghana da sauran ƙasashe kan batun basussukansu,” Jaddan ya ƙara da cewa. Hoto: Reuters / Others

Asusun Ayyukan Cigaba na Saudiyya zai sanya hannu kan wasu yarjeniyoyi na riyal biliyan biyu, kwatankwacin dala miliyan 533 da ƙasashen Afirka.

Ministan Kuɗi na ƙasar Mohammed Al-Jadaan ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis, yayin wani Taron Tattalin Arziki na Saudiyya da Ƙasashen Afirka da ake gudanarwa a birnin Riyadh.

“Muna aiki da abokan hulɗarmu don tallafa wa Ghana da sauran ƙasashe kan batun basussukansu,” Jaddan ya ƙara da cewa.

Tun da fari a wajen taron, Ministan Zuba Jari na Saudiyya Khalid Al-Falih ya ce arzikin fiye da dala biliyan 700 da ke asusun na Saudiyya, zai yi tasiri matuƙa wajen “kawo sauyi na ban mamaki” a fannin zuba jari a Afirka.

Ministan Makamashi Yarima Abdulaziz bin Salman, shi ma a wajen taron ya sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyi na farko da ƙasashen Afirka ciki har da Nijeriya da Senegal da Chadi da kuma Habasha don haɗin kai a abubuwan da suka shafi makamashi.

MAJIYA:Reuters
Rumbun Labarai
Wa yake amfana a lokacin da tattalin arzikin duniya ke ci da wuta sakamakon yaƙi?
Abubuwan da dalar Amurka Tiriliyan 1.1 mallakin Elon Musk za ta iya yi a Afirka
Elon Musk ya zama tiriloniya na farko a tarihin duniya
An zargi matatar mai mafi girma a Afirka da ƙoƙarin yin babakere game da man Nijeriya
Biliyoyin kudi da gangunan mai: Yadda matatar mai ta Dangote ke ƙarfafar Afirka da makamashi
China ta faɗaɗa janye haraji baki ɗaya ga kayan da ta shigar daga ƙasashen Afirka 53
Wasu daga waje na ƙoƙarin daƙile ci-gaban Afirka, in ji  Dangote
Ghana ta bai wa wani kamfanin ƙasar lasisin haƙar zinare kan $1bn
Shigar kuɗaɗe daga waje cikin Nijeriya don zuba jari ta ƙaru da kusan kashi 90% a 2025 – Hukumomi
Hauhawar farashin mai ta janyo aiki daga gida da karatu daga nesa a wasu ƙasashen Asiya
Harin da aka kai wa 'yan kasuwar Ghana a Burkina Faso ya sa farashin tumatur ya tashi
Naɗin 'ya'yan Dangote mata uku a manyan muƙamai: Sabon babi a tsarin gado na kasuwancin iyali
China za ta soke karɓar harajin fitar da kayayyaki daga ƙasashen Afirka 53
Me ya sa farashin zinare ke tashi a lokacin rikicin siyasa a duniya?
Gwamnatocin Afirka sun juya ga tsarin Bankin Musulunci bayan nasarar Sukuk a Benin
Ana sa ran kasuwanci tsakanin Turkiyya da Nijeriya ya kai dala biliyan 10 saboda sabbin yarjeniyoyi
Afrika na amfani da tagomashin da zinari yake samu don ƙara ƙarfin arziƙinta
Ghana ta biya basussukan dala biliyan 1.47 na fannin makashi da ake bin ta
Trump ya ce Amurka za ta karɓi gangar ɗanyen mai miliyan 50 daga Venezuela
Kamfanin Dangote ya yi watsi da ikirarin rufe matatar mansa