| Hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
NLC da TUC: Gwamnatin Nijeriya ta ce wa kungiyoyin kwadago su bi umarnin kotu na hana su tafiya yajin aiki
Wata sanarwa daga ofishin Ministan Shari'a Lateef Fagbemi ce ta ce dole NLC da TUC su bi umarnin kotu na hana su tafiya yajin aikin.
NLC da TUC: Gwamnatin Nijeriya ta ce wa kungiyoyin kwadago su bi umarnin kotu na hana su tafiya yajin aiki
Wata sanarwa daga ofishin Ministan Shari'a Lateef Fagbemi ce ta ce dole NLC da TUC su bi umarnin kotu na hana su tafiya yajin aikin. Hoto: Reuters / Others

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi kira ga ƙungiyoyin ƙwadago na ƙasar NLC da TUC su janye yajin aikin da suke shirin farawa a yau Talata a fadin kasar.

Tun a makon da jiya ne ƙungiyoyin suka ayyana tafiya yajin aiki daga ranar Talata 14 ga Nuwamban 2023.

Sai kuma a ranar Litinin 13 ga watan Nuwamba ƙungiyoyin biyu suka sake yin kira ga ma’aikata a fadin kasar cewa su ajiye ayyukan gwamnati don fara yajin aiki, a daidai lokacin da rikicin da suke yi da gwamnatin jihar Imo ke shafar ƙasar baki ɗaya.

Sai dai a wata sanarwa da mai taimaka wa Lateef Fagbemi, Ministan Shari'a na ƙasar kan watsa labarai, Kamarudeen Ogundele ya fitar a ranar Litinin da maraice, ya tuna wa ƙungiyoyin NLC da TUC batun wani umarni da kotu ta bayar na hana su tafiya yajin aikin.

"Muna so mu tunatar da Kungiyar Kwadago ta Ma'aikata da Kungiyar Kwadago ta 'Yan Kasuwa na Nijeriya cewa akwai wani umarni da kotu ta bayar na dakatar da su daga shiga yajin aikin,” in ji sanarwar.

"Shugaban Kotun Masana’antu ta Nijeriya Mai Shari’a B. B. Kanyip ne ya bayar da umarnin na wucin gadi a ranar 10 ga watan Nuwamba.

"Kotu ta bai wa ƙungiyoyin umarni, don haka, dole ne su bi umarnin da kotun ta bayar tare da miƙa kansu ga hukuma. Duk wani mataki da aka dauka wanda ya saba wa umarnin zai zama tamkar wulakanci ne ga kotu," in ji sanarwar.

Kazalika gwamnatin tarayya ta yi kira ga ƙungiyoyin ƙadagon da ma ma'aikata cewa "su girmama umarnin kotu tare da bin doka da oda."

"Muna kira ga ma'aikata da su je aiki, kuma ka da su ji tsoron komai saboda an tabbatar da tsaron su kuma za a kare su a cikin tsarin doka."

Shugabannin ƙungiyoyin sun cimma matsayar tafiya yajin aikin ne a wani taro da suka yi a Abuja a ranar Talatar makon da ya wuce, inda suka ce tuni suka fara haɗo kan mambobinsu da abokan hulɗarsu a fadin ƙasar don tafiya yajin aikin ba tare da ɓata lokaci ba.

Kungiyar kwadagon ta ɗauki matakin tafiya yajin aikin ne sakamakon “cin zarafin” shugaban NLC na kasa, Joe Ajaero, da suke zargin rundunar ƴan sanda da yi a Jihar Imo, mako biyu da suka wuce.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Ziyarar Afirka: Fiye da mutum 500,000 ake sa ran sun halarci taron ibada na Fafaroma Leo a Kamaru
Yara mata ne suka fi cutuwa daga yaƙin Sudan da aka manta da shi
Fafaroma Leo ya nufi Kamaru ƙasa ta biyu a ziyararsa ta Afirka
Yaƙi ya jefa fiye da kashi 70 cikin 100 na 'yan ƙasar Sudan cikin talauci, in ji MƊD
Yadda yakin Iran ke shafar tattalin arziki, yanki da siyasar Afirka
Za a cim ma yarjejeniyar bututun gas na Nijeriya-Maroko kan biliyan $25 a bana: Jami'i
Fafaroma Leo ya fara ziyararsa ta farko zuwa Afirka
Matsalar yunwa a Sudan: Miliyoyin mutane na cin abinci sau ɗaya a rana
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Jamhuriyar Benin
Shugaban ƙasar Djibouti Guelleh ya sake yin nasara karo na shida
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Djibouti inda Guelleh da ke mulki ke neman wa'adi na shida
Daga hanyoyin mulkin mallaka zuwa na korar mutane: Afirka da siyasar korar baƙi daga wata ƙasa
Yadda ajujuwan Afirka ke fuskantar jarrabawa mafi tsauri a duniya
Kamaru ta ce ‘yan kasarta 16 sun mutu yayin taya Rasha yaki da Ukraine
Dalilin da ya sa Kenya da Ethiopia suka zama manyan masana'antun furanni a duniya
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 15 a Angola
Senegal ta haramta wa jami'an gwamnati tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa ƙasashen waje
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina
Sudan ta yi Allah wadai da 'mummunan' harin da RSF ta kai wani asibiti yayin allurar rigakafin yara