| Hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
An saki dubban fursunoni don rage cunkoso a gidajen yarin Nijeriya
Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin fursunonin da ke gidajen yarin Nijeriya ya zarta kashi 147 na wadanda ya kamata su kasance a ciki kuma mutanen da aka tsare kan kwashe shekaru ba tare da an kammala shari'arsu ba.
An saki dubban fursunoni don rage cunkoso a gidajen yarin Nijeriya
Afonja ya kara da cewa sun soke tarar da ta kai naira miliyan 585 da aka sanya wa wasu fursunoni. / Others

An saki dubban fursunoni daga gidajen yari daban-daban a Nijeria a yunkurin gwamnatin kasar na rage cunkoso a gidajen, kamar yadda Ministan Harkokin Cikin Gida na kasar Olubunmi Tunji-Ojo ya bayyana a shafinsa na sada zumunta a karshen mako.

Wannan yana cikin kudurin shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu, wanda aka zabe shi a farkon shekarar nan, na rage cunkoson gidajen kaso, a cewar ministan.

"Jiya sun soma sakin fursunoni 4,068 cikin 80,804 da ke gidajen gyaran hali 253 a fadin kasar nan, wadanda ake tsare da su saboda sun gaza biyan tarar da aka sanya musu," in ji Olubunmi Tunji-Ojo a sakon da ya wallafa a shafinsa na X, wanda a baya ake kira Twitter.

Ya sanar da daukar matakin ne bayan ya kai ziyara gidan yarin Kuje da ke Abuja babban birnin kasar.

Kakakin ministan Ajibola Afonja ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa "fursunonin da tarar da aka sanya musu ba ta wuce ta naira miliyan daya ba ne kadai za su ci moriyar wannan shiri."

Afonja ya kara da cewa sun soke tarar da ta kai naira miliyan 585 da aka sanya wa wasu fursunoni.

Tinubu ya yi alkawarin daukar sabbin matakai na rage yawan fursunoni a gidajen yari, yana mai cewa za a rika hukunta masu laifi ta wasu hanyoyin ba tare da an garkame su ba.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin fursunonin da ke gidajen yarin Nijeriya ya zarta kashi 147 na wadanda ya kamata su kasance a ciki kuma mutanen da aka tsare kan kwashe shekaru ba tare da an kammala shari'arsu ba.

MAJIYA:TRT Afrika da abokan hulda
Rumbun Labarai
Ziyarar Afirka: Fiye da mutum 500,000 ake sa ran sun halarci taron ibada na Fafaroma Leo a Kamaru
Yara mata ne suka fi cutuwa daga yaƙin Sudan da aka manta da shi
Fafaroma Leo ya nufi Kamaru ƙasa ta biyu a ziyararsa ta Afirka
Yaƙi ya jefa fiye da kashi 70 cikin 100 na 'yan ƙasar Sudan cikin talauci, in ji MƊD
Yadda yakin Iran ke shafar tattalin arziki, yanki da siyasar Afirka
Za a cim ma yarjejeniyar bututun gas na Nijeriya-Maroko kan biliyan $25 a bana: Jami'i
Fafaroma Leo ya fara ziyararsa ta farko zuwa Afirka
Matsalar yunwa a Sudan: Miliyoyin mutane na cin abinci sau ɗaya a rana
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Jamhuriyar Benin
Shugaban ƙasar Djibouti Guelleh ya sake yin nasara karo na shida
Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Djibouti inda Guelleh da ke mulki ke neman wa'adi na shida
Daga hanyoyin mulkin mallaka zuwa na korar mutane: Afirka da siyasar korar baƙi daga wata ƙasa
Yadda ajujuwan Afirka ke fuskantar jarrabawa mafi tsauri a duniya
Kamaru ta ce ‘yan kasarta 16 sun mutu yayin taya Rasha yaki da Ukraine
Dalilin da ya sa Kenya da Ethiopia suka zama manyan masana'antun furanni a duniya
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 15 a Angola
Senegal ta haramta wa jami'an gwamnati tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa ƙasashen waje
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina
Sudan ta yi Allah wadai da 'mummunan' harin da RSF ta kai wani asibiti yayin allurar rigakafin yara