Ko Liberia ta zama abin misalin kyautata Dimokuradiyya a Yammacin Afirka?
DUNIYA
6 MINTI KARATU
Ko Liberia ta zama abin misalin kyautata Dimokuradiyya a Yammacin Afirka?Shugaban Kasar Liberia George Weah ya samu yabo da jinjina bisa yadda ya amince da kayen da abokin hamayarsa ya yi masa a yankin da sojoji suke kwace mulki da kara wa'adin zama a karaga.
An zafafa sosai a yayin gangamin zabe a Liberia. Hoto: Reuters
23 Nuwamba 2023

Daga Emmanuel Onyango

An yaba wa shugaban kasar Liberia George Weah sakamakon amincewa da shan kaye a zabe, bayan kwashe shekaru shida yana mulki sakamakon nasarar mika mulki ga farar hula a karon farko bayan yakin basasar da aka tafka.

Buga wayar da ya yi tare da taya shugaban da aka zaba Joseph Boakai ya kwantar da hankali a kasar da ake zaman dar-dar.

"Liberia ta yi nasara," in ji Weah yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a rediyo bayan sanar da sakamakon zabe.

Cigaban siyasa a Liberia abu ne da ake wa kallon sabo a tsakiya da yammacin Afirka, inda a 'yan shekarun nan sojoji suke yawan juyin mulki da kara wa'adin zaman su a kan mulkin.

"Ba abu ne da aka saba gani a wannan yankin ba a ce shugaba ya amince da ya fadi zabe. Duba da yadda aka fafata a zaben, sannan shugaba mai ci ya fito ya amince da an kayar da shi, ina tunanin wannan abun yabawa ne," in ji Adama Dempster, Sakatare Janar na Kungiyar Kare Hakkokin Dan Adam a Liberia.

Radadin yakin basasa

"Shi (Weah) ya kafa tarihi da kin aiki da tsarin siyasar Yammacin Afirka." ya fada wa TRT Afirka.

Weah dan shekara 57, tsohon dan kwallon kafa na kasa da kasa, a zagayen farko ya kara da 'yan takara 19, wanda daga nan takarar ta dawo tsakanin mutane biyu kawai. Ya sha kaye da tazarar kuri'u 20,567. A shekarar 2017 aka zabi tsohon dan kwallon na FIFA.

A tsakanin shekarun 1989 da 2003 kasar ta sha fama da yakin basasa ya yi ajalin mutane kimanin 250,000, amma a yanzu tana farfadowa a hankali tare da sharbar romon dimokuradiyya.

Dempster ya kara da cewa "Liberia ta zama kasar abar misali na kwarai da dimokuradiyya ke aiki.

"Mun yi zabuka cikin nasara tun bayan yakin basasa, kuma zabuka ne da suke na gaskiya ba tare da magudi ko wuru-wuru ba."

An samu damuwa da tsammanin afkuwar rikicin bayan zabe sakamakon arangama da aka samu tsakanin magoya bayan 'yan takara daban-daban a yayin zagaye na farko da aka gudanar a watan Oktoba. An kuma samu tashin hankali tsakanin kabilu da kauyuka.

ECOWAS ta bazama

Wannan yanayi ya zaburar da Kungiyar Yammacin Afirka ta ECOWAS, wadda ta yi gargadi kan sanar da sakamakon da ba shi ba, sannan ta gargadi masu ingiza rikici kan za ta tuhume so kan duk abu mara dadi da ya faru.

Ta yi gargadi da cewa "ECOWAS, Tarayyar Turai da Kasashen duniya za su tuhume su da alhakin duk wani abu da aka yi wanda ya janyo rikici."

Kungiyar mai kasashe 15 na Yammacin Afirka na ta kokarin daidaita kanta inda ta ke ta fama da juyin mulki a shekaru uku da suka gabata, yayin da kasashe hudu suka koma karkashin mulkin soja. Kasashen sun hada da Nijar, Mali, Burkina Faso.

A karon farko kenan da aka gudanar da zabe bayan ficewar dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, wadanda aikinsu ya kawo karshe a kasar a 2003 bayan gama yakin basasar.

Duk da cewa Liberia ta kammala zaben ba tare da rikici ba, masu fafutuka da kare hakkon dan adam na cewa har yanzu akwai rabuwar kawuna d asuke bukatar a magance su cikin kankanin lokaci.

Hadin kan Liberia

Dempster added. Dempster ya kuma ce "Ina tunanin kalubalen shi ne a hada kan dukkan 'yan kasar Liberia waje guda, a kirkiri yanayi na kula da kasa, zama tare da fara tattaunawar sulhu."

A jawabin sa na amincewa da shan kaye, Weah ya tunatar da wanda zai gaje shi cewa "'Yar karamar rata ta kuri'un da aka samu na nuni da tsananin rarrabuwar kan da ake da shi a kasarmu."

Ya kara da cewa "Mu daure mu magance wannan rarrabuwar kawuna da yakin neman zabe ya janyo, sannan mu hada kai a matsayin kasa daya al'umma daya."

Zababben shugaba mai jiran gado Boakai ya bayani tare da yin kiran da a hada kai don sake gina kasar inda ya kuma tabbatar da karbar mulki cikin nutsuwa.

A ranar Talatar nan Boakai ya bayyana cewa "An gama zabuka, kuma dole mu hada kai waje guda a matsayin al'umma don sake gina kasarmu."

Ya kara da cewa "Ina rokon dukkan 'yan Liberia, ba tare da duba ga kabila, yare, kasa, asali, addini ko 'rayin siyasa ba, a su zo mu tafi tare don kubutar da kasarmu."

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Fadan 'yan daba da gwamnati ya jawo asarar rayuka 1,200 a cikin wata uku a Haiti - MDD
Numfashi na mana wahala saboda gurbacewar iska a birnin New Delhi na India
An soke tashin jiragen sama fiye da 2,000 a Amurka yayin da harkokin gwamnati ke ci gaba da dagulewa
Zinarin da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ke shigarwa ƙasarta daga Sudan ya ƙaru yayin da ake yaƙi
COP30: Manyan masu gurbata muhalli na duniya ba su je taron sauyin yanayi na Brazil ba
Rasha ta ce tana sa ido kan Nijeriya bayan barazanar da Trump ya yi ta kai hari kasar
Zohran Mamdani: Matashi Musulmi na farko ya lashe zaɓen Magajin Birnin New York
Yadda amfani da magungunan antibiotic barkatai ya sa cututtuka suka zama makamai
Rundunar Sojin Ruwan Pakistan ta kama mugwayen ƙwayoyi na dala biliyan ɗaya a Tekun Arebiya
An gano sauro a karon farko a ƙasar Iceland
Yadda hukumomi a India suke farautar Musulmai da suke cewa 'Ina son Annabi Muhammad'
Putin ya gargaɗi Trump cewa bai wa Ukraine makamai mai linzamin Tomahawk zai jawo matsala tsakaninsu
Abin da muka sani game da mummunar arangamar kan iyaka tsakanin sojin Pakistan da Afganistan
Waiwayen 1903: An taɓa yi wa Yahudawa tayin Afirka, kamar yadda ake so a mayar da Falasɗinawa yanzu
An naɗa Sarah Mullally mace ta farko Shugabar Cocin Ingila
Yadda mutuwar ɓauna a turmutsutsu ke sauya salon farautar manyan namun dawa
An tsinci gawar jakadan Afirka ta Kudu a Faransa a wajen otal a birnin Paris
Babban Alkalin Kotun Amurka ya dakatar da umarnin Trump na korar ma’aikatan VOA
UNGA: Yadda ta kaya a taron 'nuna wa juna yatsa da huce haushi' na Majalisar Dinkin Duniya
Yadda jami'an diflomasiyyar duniya suka fice daga Zauren UNGA yayin da Netanyahu zai yi jawabi