| Hausa
DUNIYA
2 MINTI KARATU
Yunwa da kishirwa na yi wa Falasdinawa 500,000 barazana
Hare-haren da Isra'ila ta kwashe sama da wata biyu tana kaiwa a Gaza sun yi sanadin mutuwar Falasdinawa fiye da 17,487, galibinsu mata da kananan yara sannan fiye da mutum 46,480 sun jikkata.
Yunwa da kishirwa na yi wa Falasdinawa 500,000 barazana
Ana fama da karancin kayayyakin abinci da ruwan sha a Gaza sakamakon hare-haren Isra'ila. / Hoto: Reuters / Others
9 Disamba 2023

1550 GMT — Yunwa da kishirwa na yi wa Falasdinawa 500,000 barazana

Falasdinawa dubu 500 ke cikin barazanar yunwa da kishirwa a biranen da hare-haren Isra’ila ke kara karuwa, kamar yadda gwamnatin Gaza ta bayyana.

Gwamnatin ta Gaza ta ce jama’ar birnin na cikin bala’i sakamakon dagangan Isra’ila ke kai hare-hare kan ababen more rayuwa da ke da alaka da abinci da ruwa.

Mai magana da yawun birnin, Hosni Muhanna ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu a ranar Asabar cewa karancin man fetur yana kawo cikas wurin kwasar wadanda suka samu rauni da kuma jigilar gawawwaki.

1025 GMT — Isra'ila na ci gaba da zafafa hare-hare a Gaza bayan Amurka ta ki amincewa da kudurin

Isra’ila ta ci gaba da zafafa kai hare-hare a Gaza bayan Amurka ta yi fatali da kudurin da aka gabatar ga Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya wanda zai bayar da dama a tsagaita wuta a hare-haren da Isra'ila take kaiwa Gaza.

Hamas da hukumomin Falasdinu sun yi Allah wadai da wannan matakin na Amurka a daidai lokacin da ma’aikatar lafiya ta Gaza ta sanar da cewa mutum 17,487 suka mutu a Gaza, akasari mata da yara.

Haka kuma wani hari da Isra’ila ta kai a kudancin birnin Khan Yunis ya kashe mutum shida, inda wasu biyar suka mutu a wani hari na daban a Rafah, kamar yadda ma’aikatar ta tabbatar a ranar Asabar.

MAJIYA:AA, AFP, AP, Reuters
Rumbun Labarai
Chadi za ta tura sojoji 750 domin yaƙar 'yandaban Haiti
Trump: Amurka na duba yiwuwar 'kammala' hare-haren soji kan Iran
NATO na fuskantar ‘mummunar makoma’ idan ƙasashenta suka ƙi taimaka wa Amurka a yaƙin Iran - Trump
Trump ya ce bai shirya yin yarjejeniya ba domin kawo ƙarshen yaƙin Iran
Tsarin kiwon lafiya a Gabas ta Tsakiya na fuskantar barazana yayin da rikici ke ƙara muni: WHO
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya
Mashigar Hormuz: Hanyar ruwan da za ta iya girgiza tattalin arzikin duniya
Dalilai huɗu da suka sa matasan Afirka suka fi lafiyar ƙwaƙwalwa a duniya
Musulmai a Turkiyya, Oman, Singapore, da Australia za su fara azumin Ramadan a ranar Alhamis
'Babu wani takamaiman abin da aka cim ma' a ganawar Trump da Netanyahu a kan Iran
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba
Trevor Noah: Trump ya yi barazanar maka mai gabatarwa a Gasar Grammy a Kotu
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran