| Hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
‘Yan bindiga sun kashe wasu mutane a Nijar
"’Yan ta’adda a kan babura da dama sun kai hari a kauyukan Amara da Loudji," masu nisan kilomita 30 a kudu maso gabashin Bankilare, "inda suka kashe mutum 11," in ji sanarwar.
‘Yan bindiga sun kashe wasu mutane a Nijar
Ranar 17 ga watan Disamba, shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya ce kasar tana "samun ci-gaba" wajen magance matsalar tsaro./Hoto:Ofishin Shugaban Mulkin Sojin Nijar / Others

Mutum goma sha daya ne suka mutu a hare-haren da wasu ‘yan bindiga suka kai a kauyuka biyu na Jamhuriyar Nijar da ke kan iyaka da Burkina Faso a karshen mako, a cewar sanarwar da ma’aikatar tsaron kasar ta fitar ranar Lahadi.

"’Yan ta’adda a kan babura da dama sun kai hari a kauyukan Amara da Loudji," masu nisan kilomita 30 a kudu maso gabashin Bankilare, "inda suka kashe mutum 11," in ji sanarwar.

Sun kai harin ne a yayin da jami’an tsaron Nijar suka “kaddamar da jerin hare-hare” ranar Juma’a, wadanda ma’aikatar tsaron ta ce “sun lalata daukacin” hanyoyin sadarwar ‘yan ta’addan.

Ta kara da cewa an kashe soja daya tare da jikkata guda biyar ranar Juma’a lokacin da motarsu da ke yin sintiri ta taka nakiya a kauyen Ouro Gueladjo, mai nisan kilomita 70 daga Yamai, babban birnin kasar.

Labari mai alaka: Nakiya ta kashe sojoji bakwai a Jamhuriyar Nijar

Tun daga watan Yuli sojoji suke mulki a Nijar bayan sun kifar da gwamnatin farar-hula.

Ranar 17 ga watan Disamba, shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya ce kasar tana "samun ci-gaba" wajen magance matsalar tsaro, yana mai cewa sojoji sun samu “nasarori da dama” ta hanyar dakile tarzoma.

Sojoji da mazauna yankunan da ke kan iyaka da Burkina Faso da Mali sun ce an samu kwanciyar hankula a makonnin da suka gabata.

A watan Oktoba an kashe sojoji shida a kan iyakar Nijar da Burkina Faso sakamakon ba-ta-kashi da ‘yan bindiga.

Kazalika a watan na Oktoba, an kashe sojojin Nijar 29 a hari mafi muni da ‘yan bindiga suka kai musu tun bayan juyin mulkin da soji suka yi.

MAJIYA:AFP
Rumbun Labarai
Gwamnatin Mali ta tabbatar da kashe sojoji 30 a wani harin ta'addanci a arewacin ƙasar
Aikin matatar man Dangote zai ci gaba a gaɓar tekun  Kenya, a cewar Shugaba Ruto
Afirka ta sami tallafin $900m domin faɗaɗa fasahar girki na zamani mara gurɓata muhalli
Rasha na son ƙarfafa alaƙa da Ƙawancen Ƙasashen Sahel (AES) - Lavrov
Sojojin Sudan sun ƙwace ƙauyen Al-Kurmuk bayan arangama da dakarun RSF
Jami'an tsaro a Afirka ta Kudu sun kama masu haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba fiye da 200
Ƙawancen tsaro na Turkiyya da Afirka na haɓaka a tsarin duniya da ke sauyawa
Jami’an leken asiri sun lalata yunƙurin ‘yan ta’addan Daesh na kai hari a garuruwan Morroco bakwai
'Yansandan Afirka Ta Kudu sun ce mutuwar ɗan Nijeriya ba ta da alaƙa da tashin hankalin ci-rani
MDD ta yi gargaɗin cewa hare-haren RSF na iya mayar da birnin Al-Obeid na Sudan kamar Al-Fasher
Rikicin diflomasiyya ya kaure tsakanin Ghana da Afirka ta Kudu kan mutuwar ɗan Ghana
Burkina Faso, Mali da Nijar sun gabatar da sanarwar ficewa daga ICC, in ji kotun
Sojojin Mali sun raka motocin dakon mai da abinci 940 zuwa Bamako saboda fargabar harin ta'addanci
Sojojin Burkina Faso sun ce sun kashe 'yanta'adda fiye da 400 a wani hari da suka daƙile
An gurfanar da ɗalibai mata takwas a kotu a Kenya kan zargin kisan abokan karatunsu a gobara
Yadda Nijeriya ke fama da hauhawar farashin gas din girki
MDD ta yi gargaɗin cewa cutar Ebola na iya jefa kusan mutane miliyan 1 cikin talauci a DRC
Afirka ta Kudu ta mai da fiye da mutum 25000 kasashensu kafin wa'adin 30 ga Yuni na masu ƙyamar baƙi
Yadda abinci ke yin kisan mummuƙe a Afirka
Burkina Faso ta kawo ƙarshen dangantakar diflomasiyya da Faransa