| Hausa
AFIRKA
4 MINTI KARATU
Sierra Leone ta bar tsohon shugaban kasar Koroma ya tafi jinya Nijeriya
Za a bar Ernest Bai Koroma ya tafi Nijeriya tsawon watanni uku don duba lafiyarsa, a cewar kotu.
Sierra Leone ta bar tsohon shugaban kasar Koroma ya tafi jinya Nijeriya
Ernest Bai Koroma ya yi mulkin kasar saliyo tsakanin shekarar 2007 zuwa 2018. Hoto / AA       / Others

Wata babbar kotun Saliyo a ranar Laraba ta bai wa tsohon shugaban kasar Ernest Bai Koroma, wanda ake tuhumarsa da laifin cin amanar kasa a wannan wata damar tafiya Nijeriya don a duba lafiyarsa.

Ana tuhumar Koroma mai shekaru 70 da laifuka hudu, ciki har da zargin hannu a yunkurin da sojoji suka yi na hambarar da gwamnatin kasar a watan Nuwamba.

Ana fargaba cewa tuhumar da ake yi wa Koroma na da nasaba da tashin hankali da ya barke bayan zaben kasar na watan Yunin 2023 inda aka sake zaben shugaba Julius Maada Bio a wa'adi na biyu.

Babban dan takarar adawa a zaben ya ki amincewa da sakamakon zaben sannan wasu kasashen waje sun nuna shakku kan sakamakon zaben.

Dakile nasarar juyin mulki

Bayan wasu watanni, a ranar 26 ga watan Nuwamba, wasu ‘yan bindiga sun kai hari a barikin soji da wani gidan yari da kuma wasu yankuna na kasar ta Saliyo, inda suka ‘yantar da fursunoni kusan 2,200 tare da kashe mutane sama da 20.

Bayan haka ne gwamnati ta ce juyin mulki ne da aka yi nasarar dakilewa wanda akasarin masu gadin Koroma suka jagoranta. An gayyaci tsohon shugaban kasar domin amsa tambayoyi a farkon watan Disamba.

Koroma ya yi Allah wadai da harin jim kadan bayan faruwar lamarin, kana lauyoyinsa sun kira tuhumar da ake yi masa da "zargi mara tushe kuma wani bangare na "bangar siyasa".

A ranar Laraba ne alkalin da ke shari'ar ya yanke hukuncin da ya bai wa lauyoyin Koroma nasara kan bukatar neman kotun ta ba shi damar tafiya zuwa kasar waje saboda duba lafiyarsa.

Tafiya zuwa Nijeriya

Za a bar tsohon shugaban kasar ya tafi Nijeriya har na tsawon watanni uku, a cewar alkalin kotun kafin daga bisani ya dage sauraron karar zuwa ranar 6 ga watan Maris.

Kawo yanzu babban alkalin-alkalai na Saliyo ya ki cewa komai kan batun.

A yayin wannan hukunci Koroma bai gurfana a gaban kotu ba a ranar Laraba, a cewar wani wakilin Reuters.

An ba da belinsa ne a lokancin da kotu ta tuhume shi a ranar 3 ga watan Janairu, kuma an tabbatar da cewa ana tsare da shi a gidansa da ke Freetown babban birnin kasar.

A baya Nijeriya ta yi tayin karbar bakoncinsa na wucin gadi, wanda shi kansa ya amince da hakan, a cewar wata wasika daga kungiyar raya tattalin kasashen yammacin Afirka ECOWAS, wadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani.

A cewar kundin hukunta manyan laifuka na Saliyo, mutumin da aka samu da laifin cin amanar kasa zai iya fuskantar daurin rai da rai.

Ana kuma tuhumar wasu mutane 12 da laifin cin amanar kasa dangane da juyin mulkin da bai yi nasara ba, ciki har da tsoffin jami'an 'yan sanda da jami'an gidajen gyara hali da kuma wani jami'in tsaro na Koroma.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Fiye da mutum 7,000 sun kamu da annobar Ebola a Jamhuriyar Kongo
Shugaban Nijar ya naɗa Birgediya Janar Mamane Sani Kiaou a matsayin sabon shugaban hafsan sojoji
FIFA ta musanta iƙirarin Maroko na 'karɓar baƙuncin' wasan ƙarshe na Gasar Kofin Duniya na 2030
Majalisar Sudan ta cire 'yantawayen RSF daga tattaunawar ƙasa
An raba mutane fiye da 4,500 da gidajensu a Darfur ta Kudu da Blue Nile saboda matsalar tsaro
An ceto fiye da 'yan ci-rani 1,000 kusa da tekun yammacin Afirka cikin mako ɗaya, in ji MSF
Shugaban Zambia Hichilema ya yi farin ciki da masoyan da suka ba shi kyautar kazar gida
Gwamnatin Ghana ta kashe $4.37m don kwashe 'yan ƙasarta daga Afirka ta Kudu
Gwamnatin Nijar ta yi kira ga jama'a su duƙufa da Al-Ƙunut domin neman tsari daga 'maƙiyan ƙasa'
Kwalara ta kashe mutum 23 a Sudan, fiye da 310 sun kamu da cutar
Majalisar Dinkin Duniya ta amince a sake zana taswirar Afirka zuwa ainihin yadda nahiyar take
Nijar na zargin Faransa da tunzura sojojin da suka yi yunkurin tawayen da aka dakile
Tallafin ƙasashen waje da harin jiragen sama marasa matuƙa sun ƙara tsananta yaƙin Sudan - MDD
Babban hafsan sojin Sudan Burhan na rangaɗi game da shirin yaƙi a fagen yaƙin Blue Nile
Dubban mutane sun yi zanga-zanga don nuna goyon bayansu ga sojin Nijar bayan dakile yunƙurin tawaye
Hatsarin mota a Masar ya yi ajalin mutum 16 a sanannen yanki mai cike da ‘yan yawon bude ido
Shugaban ƙungiyar Tarayyar Afirka ya yi Allah wadai da boren da aka yi a Nijar
An kama ‘yar jarida mai yawan mabiya Denise Dusauchoy ‘yar kasar Kongo a Tanzania
Tebboune ya sake bayyana goyon bayan Aljeriya ga Nijar yayin da ake fuskantar barazanar tsaro
Yadda maganin rana guda zai iya kawo ƙarshen cutar bacci a Afirka