Gwamnan Yankin Tahoua a Jamhuriyar Nijar, Souleymane Amadou Moussa, ya kai ziyara a ranar Litinin zuwa Sansanin Sojin Sama na 401 da ke Filin Jirgin Sama na Tahoua, bayan wani hari da wasu ’yanbindiga suka kai da daddare wanda dakarun tsaro suka samu nasarar daƙilewa.
Gwamnan, tare da rakiyar shugabannin hukumomin tsaro na yankin da kuma mambobin Kwamitin Tuntuɓa na Sabunta Tsarin Mulki, sun yi kewaye sansanin domin duba irin ɓarnar da aka yi tare da yaba wa jami’an tsaro kan saurin mayar da martani.
Harin ya faru ne da misalin karfe 3:05 na asuba agogon yankin, lokacin da wasu ’yanbindiga da suka iso kan babura suka yi yunkurin kai farmaki kan filin jirgin. A cewar jami’ai, maharan sun samu damar lalata wasu garejin ajiye jirage marasa matuƙa kafin jami’an tsaro su fatattake su.
Hukumomi sun ce a yayin artabun, dakarun ƙasar kaɗan sun samu raunuka, yayin da aka kashe wasu daga cikin maharan. Haka kuma an kama mutane biyar da ake zargi, da taimakon mazauna yankin. Jami’an tsaro sun ce an kwato kuɗi masu yawa da wasu kayayyaki daga hannun waɗanda ake zargin.
A yayin ziyarar, gwamnan da tawagarsa sun duba wuraren da harin ya shafa a filin jirgin, ciki har da wuraren aiki na jami’an tsaro da shingen tsaron da maharan suka yi ƙoƙarin kutsawa.
Daga nan tawagar ta wuce zuwa Hedikwatar Rundunar ’YanSanda ta Yanki (DRPN), inda ake tsare da mutanen biyar da aka kama.
Da yake magana bayan ziyarar, Gwamna Moussa ya ce manufar ziyarar ita ce duba halin da ake ciki bayan harin. Ya tabbatar da cewa duk da cewa wasu kayayyaki an lalata su amma ba sosai ba, martanin da dakarun tsaron suka mayar ya tilasta wa maharan janyewa cikin gaggawa.
Ya ce jami’an tsaron sun samu nasarar kashe wasu daga cikin maharan tare da kama biyar.
A madadin hukumomin ƙasar, gwamnan ya taya dakarun tsaron murna kan ƙwarewarsu da kuma saurin ɗaukar mataki.
Ya kuma tabbatar wa al’ummar ƙasar da na duniya cewa an shawo kan lamuran a halin yanzu. A cewarsa, rayuwa a Tahoua na tafiya kamar yadda aka saba, filin jirgin sama na ci gaba da aiki cikin tsaro, kuma duk ayyukan filin jirgin suna gudana ba tare da tangarɗa ba.
Gwamna Moussa ya kuma yi kira ga mazauna yankin da su kasance cikin shiri da kula tare da taimaka wa jami’an tsaro ta hanyar sanar da su duk wani abu da ya zama abin zargi.
Ya tunatar da jama’a cewa akwai lambobin waya kyauta da za su iya kira domin sanar da duk wata barazana, ta yadda jami’an tsaro za su iya daukar mataki cikin gaggawa.
Hukumomi sun tabbatar da cewa an kaddamar da bincike kan wannan lamari, yayin da ayyukan tsaro ke ci gaba a yankin.









