| Hausa
DUNIYA
3 minti karatu
Trump: Za a kai wa tashoshin lantarki da gadojin Iran hari idan ba a buɗe Mashigar Hormuz ba
Trump ya kuma ce Amurka ta ceto wani memban ma'aikatan jirgin F-15 “wanda ya ji rauni sosai kuma jarumi" daga "surƙuƙin tsaunukan Iran."
Trump: Za a kai wa tashoshin lantarki da gadojin Iran hari idan ba a buɗe Mashigar Hormuz ba
Trump ya kira jami'in da aka ceto 'Kanal mai matukar daraja,' yana mai cewa ba kasafai ake yin irin waɗannan ayyukan ba saboda haɗari ga 'mutane da kayan aiki.' / AFP

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazana a cikin wani rubutu cike da zage-zage a dandalin sada zumunta a ranar Lahadi, cewa zai kai hari kan tashoshin samar da wutar lantarki da gadajoji a Iran idan ba a buɗe Mashigar Hormuz ba washegari.

Bayan wa'adin awanni 48 da ya bayar a ranar Asabar, Trump ya rubuta a shafinsa na Truth Social cewa "Talata za ta kasance Ranar Tashoshin Wuta, da Ranar Gada, duka a cikin rana guda, a Iran. Ba a ga rana irinta ba!!!"

"Ku buɗe wannan Mashigar fa, ku mahaukatan banza, in ba haka ba za ku kasance cikin balbalin bala’i - KAWAI KU JIRA" in ji shugaban, sannan ya ƙara da cewa: "Alhamdulillah."

Trump ya ce kuma Amurka ta ceto wani memban ma'aikatan jirgin F-15 “wanda ya ji rauni sosai kuma jarumi daga surƙuƙin tsaunukan Iran."

Masu AlakaTRT Afrika - Amurka ta ceto direban jirgin F-15 na biyu da ake nema a Iran — Trump

Ya ce jami'in da aka ceto "kanal ne da ake matuƙar girmamawa," sannan ya ƙara cewa irin wannan aiki "ba a fiye yin irinsa ba saboda haɗari ga rayuka da kayan aiki."

"Hari na biyu ya biyo bayan na farko, inda muka ceto matukin jirgi ido na ganin ido, abin da ba a saba gani ba, mun shafe awanni bakwai a sama a Iran. Wani ABIN MAMAKI na nuna jarumtaka da ƙwarewa daga kowa!" in ji shi.

"Zan yi taron manema labarai tare da sojoji a Ofishin Oval, ranar Litinin da karfe 1:00 na rana," kamar yadda ya ƙara bayyanawa.

Tun da farko Trump ya faɗa a ranar Lahadi cewa Amurka ta ceto wani jami'in soja a cikin "daya daga cikin mafi jarumtakar ayyukan Bincike da Ceto a tarihin Amurka."

Ya bayyana cewa jami'in ya ji rauni, Trump ya ce zai "warke lafiya."

Ya ce aikin ya biyo bayan wani ceto na daban na wani matukin jirgin Amurka a ranar Juma'a, wanda ba a sanar da shi da wuri ba don kada a yi ƙafar angulu ga aikin na biyu.

Tashin hankali a yankin ya ƙaru tun lokacin da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar da wani farmaki tare kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya kashe sama da mutane 1,340 zuwa yanzu, ciki har da tsohon jagoran addini na ƙasar Ali Khamenei.

Tehran ta mayar da martani da harin jiragen sama marasa matuka da harin makamai masu linzami a kan Isra'ila, haka nan kan Jordan, da Iraki, da ƙasashen Gulf da ke masaukin kadarorin sojin Amurka. Iran ta kuma takaita zirga-zirgar jiragen ruwa ta hanyar Mashigar Hormuz.

Rumbun Labarai
UAE ta fita daga Ƙungiyar Ƙasashe Masu Arzikin Fetur ta Duniya, OPEC
Waye zai zama Sakatare Janar na MDD? Macky Sall na fuskantar abokan takara daga Latin Amurka
Abubuwan da muka sani game da harbe-harben da aka yi a taron liyafar Trump da manema labarai
Trump ya ce harbin da aka yi ba zai hana shi samun nasara a yakin Iran ba
An fitar da Trump daga wajen liyafa da 'yanjarida yayin da 'wata kara' ta haifar da fargabar tsaro
Gagarumar gobara ta laƙume gidaje 1,000 a ƙauyen da ke kan ruwa, tare da raba dubbai da muhallansu
'Gigitaccen mahaukaci': Sanatocin Amurka sun caccaki barazanar Trump ga Iran a matsayin laifin yaƙi
Mai Bai wa Trump Shawara kan Addini tana shan raddi bayan ta kwatanta shi da Yesu Almasihu
Damuwar 'yan Republican na ƙaruwa gabanin zaɓukan rabin wa'adi saboda tasirin yaƙin Iran
Chadi za ta tura sojoji 750 domin yaƙar 'yandaban Haiti
Trump: Amurka na duba yiwuwar 'kammala' hare-haren soji kan Iran
NATO na fuskantar ‘mummunar makoma’ idan ƙasashenta suka ƙi taimaka wa Amurka a yaƙin Iran - Trump
Trump ya ce bai shirya yin yarjejeniya ba domin kawo ƙarshen yaƙin Iran
Tsarin kiwon lafiya a Gabas ta Tsakiya na fuskantar barazana yayin da rikici ke ƙara muni: WHO
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya
Mashigar Hormuz: Hanyar ruwan da za ta iya girgiza tattalin arzikin duniya
Dalilai huɗu da suka sa matasan Afirka suka fi lafiyar ƙwaƙwalwa a duniya
Musulmai a Turkiyya, Oman, Singapore, da Australia za su fara azumin Ramadan a ranar Alhamis
'Babu wani takamaiman abin da aka cim ma' a ganawar Trump da Netanyahu a kan Iran
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba