| Hausa
TURKIYYA
4 MINTI KARATU
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan ya gana da takwarorinsa gabanin Taron Diflomasiyya na Antalya
Dubban mahalarta taron difomasiyya da 'yan siyasa da ɗalibai da malaman jami'a da ƙungiyoyin fararen-hula sun halarci taron diflomasiyya mai taken Antalya Diplomacy Forum, a ƙarƙashin shirin Elevating Diplomacy Amidst Crises.
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan ya gana da takwarorinsa gabanin Taron Diflomasiyya na Antalya
Ministocin Harkoki Wajen Turkiyya da Kazakhtan sun tattauna kan harkokin yankin da kuma haɗa gwiwa don ci-gaban ƙasashen yankin Turkiyya na Turkic Council. / Hoto: AA / Others

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya gana da takwarorinsa na Kazakhstan da Iraƙi da Lebanon da Gambiya da Tijikistan gabanin babban taron diflomasiyya na Antalya Diplomacy Forum wanda za a yi tsakanin ranar 1 zuwa 3 ga Maris.

Fidan da Ministan Harkokin Wajen Kazakhtan Murat Nurtleu sun tattauna kan dangantakar da ke tsakaninsu da kuma matakan da za su ɗauka na kyautata alakarsu a fannin tsaro ranar Ahamis.

Wasu majiyoyin diflomasiyya sun rawaito cewa ministocin biyu sun kuma tattauna kan yadda za su bunƙasa dangantakarsu a fannin ilimi da al'adu.

A lokacin ganawar tasu, sun ce ƙawancen da suka ƙulla kan kasuwanci inda suka yi hasashen zai kai na dala biliyan 10, yanzu ya zarta.

Ministocin biyu sun yi tattaunawa kan ayyukan da suke gudanarwa game da ci-gaban cinikayya da makamashi da sufuri.

Kazalika, Fidan da Nurtleu sun yi tsokaci kan harkokin ci-gaban yankinsu da kuma buƙatar haɗin-kai don ƙarfafa Majalisar Ƙasashen yankin Turkiyya wato Turkic Council.

Tattaunawa kan shirin Shugaba Erdogan na ziyartar Iraƙi

Lokacin da yake ganawa da takwaransa na Iraƙi Fuad Hussein, sun tattauna kan shirin shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan na kai ziyara ƙasarsu.

Bayan wani taro da aka yi tsakanin Turkiyya da Iraƙi a Ankara a watan Disamba, Fidan da Hussein sun tattauna kan shirin wannan taro da ake sa ran gudanarwa a birnin Bagadaza nan ba da jimawa ba.

Taron zai mayar da hankali kan yanayin tsaron Iraƙi da ci-gaban yankin da kuma wani shirin gina hanyoyi mai taken Development Road Project.

Samar da ci-gaba a Gaza

Fidan ya gana da takwaransa ministan Harkokin Wajen Lebanon Abdallah Bouhabib don tattauna kan abubuwan da suka shafi kasashen biyu da kuma batun kawo ci gaba a Gaza.

Yayin tattaunawar, ministocin harkokin wajen biyu sun yi magana kan batun tsaro da zaman lafiya a Gaza da sauran yankin.

Ganawa da ministocin harkokin wajen Gambiya fa na TajikistanKazalika Fidan ya gana da ministan Harkokin Wajen Gambiya Mamadou Tangara da na Tajikistan Sirojiddin Muhriddin.

Babban jami’in harkokin diflomasiyyar Turkiyya ya bayyana jin dadinsa dangane da nasarorin da aka samu ta fuskoki da dama da Gambiya wacce daya daga cikin manyan kawayen Turkiyya ne a Afirka.

Kasashen biyu sun amince su karfafa huldarsu ta fuskar tsaro da tattalin arziki da al’adu.

Yayin ganawarsa da Muhriddin, an shirya manyan ziyarce-ziyarce a gaba daya shekarar kuma an dauki manyan matakai don karfafa hulda a fannin tsaro da ilimi da tattalin arziki.

Dangane da batun bayanan fa Muhriddin ya samar kan shata iyaka tsakanin Tajikistan da Kyrgyzstan, Fidan ya bayyana gamsuwar Turkiyya kan nasarar da aka samu ta wannan fuskar kuma yarjejeniyar da aka samu kuma ya ce yarjejeniyar da aka samu za ta taimaka wajen samar zaman lafiya da ci gaba a yankin.

Wakilai daga ƙasashe 147

Taron Diflomasiyya na Antalya zai karɓi baƙuncin wakilai daga ƙasashe 147.

Mutum kusan 4,500 ake sa rai za su halarci taron, ciki har da shugabannin ƙasashe 19 da ministoci 73 da wakilan ƙungiyoyin ƙasashen duniya 57.

Taron zai mayar da hankali kan batutuwa da suka haɗa da sauyin yanayi da ƙaura da yaƙi da ƙyamar Musulunci da ƙirƙirarriyar basira.

Mutum kusan 2,000 ne suka halarci taron a shekarar 2021. Kazalika, a 2022, an yi ƙananan taruka 30 daga cikin babban taron, yayn da a bana ake sa rai za a yi ƙananan taruka 52.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Jiragen ruwa biyu na kasuwanci sun yi karo a gabar Tekun Silivri a Istanbul, mutum 10 sun ɓata
30 ga Agusta: Nasarar da ta buɗe hanyar tasowar Turkiyya ta zamani
An haƙo wani sassaƙen ɗan'adam zaune a kan damisa mai shekaru 11,000 a Turkiyya
Turkiyya ta ƙara haɓaka kasuwancin da take yi da ƙasashen Musulmi
Aselsan: Kamfanin tsaro na Turkiyya zai baje-kolin jirgin ƙarƙashin ruwansa a bikin Teknofest
Turkiyya ta ƙaddamar da shirin 2026–2030 na zama cibiyar fasahar AI ta duniya
Trump ya yi 'murna' kan yarjejeniyar tsaro ta Makka da Turkiyya da Pakistan da kuma Saudiyya suka yi
Shugaba Erdogan ya jinjina wa shekara 25 na Jam'iyyar AK kan samar da 'sauyi mai tarihi' a Turkiyya
Shekaru 25 na Jam’iyyar AK da matsayin Turkiyya na mai taka rawa a yanki da ma duniya
Ministan Harkokin Wajen Masar ya gode wa Turkiyya saboda tarban karamci da ta yi wa Mohamed Salah
Turkiyya ta yi kira ga Tunisia da ta saki jagoran Ennahda Ghannouchi da ke tsare a kurkuku
Turkiyya ta kama mutum 30 a wani samame da aka kai kan ƙungiyar masu aikata laifuka ta Alihan
Turkiyya za ta ci gaba da taka rawa da kuma shiga tsakani a Libya, in ji Ministan Harkokin Waje
Cikin hotuna: Turkiyya ta haskaka muhimman wurare don murnar Yajejeniyar Tsaron Hadin Gwiwa ta Makka
An fara gasar baje-kolin jiragen sama marasa matuka ta TEKONOFEST a garin Sirnak na Turkiyya
Erdogan zai kai ziyara Saudiyya don tattaunawa da Mohammed bin Salman da Firaministan Pakistan
Shugaban sadarwa na Turkiyya ya ce Isra'ila na yi wa yunƙurin zaman lafiya na Gaza zagon ƙasa
Turkiyya ta kama ɗanta'addan FETO da ake nema bisa yunƙurin kashe Shugaba Erdogan a shekarar 2016
Turkiyya ta yi fice a Gasar Duniya ta Rubutu a Kwamfuta da kambi 36
Turkiyya da Nijeriya sun ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa kan ƙera jiragen ruwa