| Hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
Kotu a Ghana ta yanke wa wasu ƴan a-ware hukuncin ɗaurin shekara 17 a gidan yari
Babbar Kotun birnin Accra a Ghana ta yanke wa wasu 'yan aware hudu hukuncin daurin shekaru 17 a gidan yari bisa samun su da laifin gudanar da haramtacciyar kungiya.
Kotu a Ghana ta yanke wa wasu ƴan a-ware hukuncin ɗaurin shekara 17 a gidan yari
Wadanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da tsofaffin jami'an ƴan sanda da na soja. / Hoto: Getty Images / Others

Wata Kotu a Accra babban birnin kasar Ghana ta yanke hukuncin daurin shekaru 17 ga wasu manyan jami'an ƙungiyar 'yan a-ware ta Western Togoland Restoration Front (WTRF), ɗaurin shekara 17 a gidan yari.

Hukuncin nasu da aka yanke a ranar Laraba ya zo ne bayan da Mai Shari’a Mary Maame Ekueh Nyanzuh ta Babbar Kotun birnin Accra ta samu mutanen hudu da laifuka da dama.

Wadanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da tsofaffin jami'an ƴan sanda da na soja.

Zarge-zargen da ake tuhumarsu da shi sun haɗa da: kasancewa mambobin haramtacciyar kungiya da kiran taron haramtacciyar kungiya da halartar taro, da bayar da gudunmawa don amfanin haramtacciyar kungiya.

Neman sassauci

An yanke wa wanda ya kafa ƙungiyar WTRF, Michael Koku Kwabla, wanda aka fi sani da Togbe Yesu Edudzi, daurin shekaru biyar a gidan yari, da kuma tarar cedi na Ghana 12,000 kwatankwacin dala 940.

Sauran mutane ukun da ake zargin Nene Kwaku da Emmanuel Afedo, da Abednego Mawena, an yanke musu hukuncin daurin shekaru hudu a gidan yari kowanne, da kuma tarar cedi 4,800, kwakwatancin dala 375 kowanne.

Lauyan da ke kare Andy Vortia ya roki a sassauta hukunce-hukuncen da ake yi wa wadanda yake karewa, yana mai cewa tuni suka shafe shekaru uku a tsare.

Masu gabatar da ƙara, karkashin jagorancin Joshua Sackey, sun yi adawa da ƙarar sassaucin hukuncin, inda suka bukaci kotun da ta zartar da hukunci mai tsauri don daƙile masu son aikata irin wannan laifin.

Hare-hare a arewaci

A ranar 25 ga Satumba, 2020, mambobin WTRF sun tare tituna a arewacin Ghana tare da ƙona wasu motocin jama'a guda biyu.

A ranar ne wasu ‘yan kungiyar suka kai hari a ofisoshin ‘yan sanda da ke yankin tare da kuɓutar da wadanda ake tsare da su.

WTRF kungiya ce da ta ɓalle daga Gidauniyar Nazarin Gida, wacce babbar manufarta ita ce ɓallewa daga Jamhuriyar Ghana, da kafa kasa mai cin gashin kanta.

Kungiyar dai na neman iko da yankunan Oti da Volta a arewacin kasar, da kuma gabashin kasar Ghana.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Mali ta ɗaure jami'in diflomasiyyar Faransa shekara 20 a gidan yari kan zargin neman haddasa rikici
Fafutukar samar da kiwon lafiyar bai-ɗaya a Afirka
An yi wa jagoran 'yan adawa na Guinea Bissau ɗaurin talala
Ƙishirwa ta kashe mutum 49 a saharar Nijar bayan motarsu ta lalace
Mali ta haramta hawa babura a wajen birane saboda hare-haren ta'addanci
Tawagar kwallon DRC na neman abokiyar karawa bayan Sifaniya ta fasa buga wasa da su saboda Ebola
'Yan Nijeriya da Mozambique da Laberiya na cikin mutum  21 da gobarar otel ta kashe a New Delhi
Shugaban Nijar Abdourahamane Tiani ya fara ziyarar aiki a Turkiyya
Nijar da Benin sun ƙaddamar da kwamitin da zai sa ido kan iyakokin ƙasashen biyu
Manyan attajiran Afirka da kuma nauyin talaucin da nahiyar ke fama da shi
Malawi za ta kwashe 'yan ƙasarta daga Afirka ta Kudu saboda matsalar rikicin ƙyamar baƙi
Dalibai tara sun gurfana a gaban kotu kan tayar da gobara a wata makaranta a Kenya
Mutane da yawa sun fito da wuri don kaɗa kuri'a a babban zaben Habasha
Shugaban WHO ya ziyarci cibiyar Ebola yayin da cutar ke ƙara ƙamari
Amurka ta aike wa Nijar kayan aikin soja da darajarsu ta kai dala miliyan 2.3 duk da takun-saƙa
Ɗalibai 16 sun rasu sakamakon gobara a wata makarantar 'yanmata a Kenya
Ghana ta kwashe 'yan ƙasarta 300 daga Afirka ta kudu yayin da ake zanga-zanga kan baƙin haure
Mutane uku sun mutu bayan motar fasinja ta yi karo da giwa a gandun dajin Uganda
Shugaban Senegal Faye ya naɗa sabon firaminista da zai maye gurbin Sonko
Adadin mutanen da Ebola ta kashe a Jamuhuriyar Kongo ya wuce 200