TURKIYYA
3 MINTI KARATU
Hukumar ba da agaji ta Turkiyya ta kai wa Falasɗinawa kayan agaji a watan Ramadan
Hukumar hadin kai ta Turkiyya TIKA za ta ci gaba da kasancewa tare da al'ummar Falasdinu, in ji jami'in hukumar.
Hukumar ba da agaji ta Turkiyya ta kai wa Falasɗinawa kayan agaji a watan Ramadan
Hukumar ba da agaji ta Turkiyya ta kai kayan abinci na watan Ramadan ga ma'aikatar Waƙafi da Harkokin Addini ta Falasdinu da za a raba wa iyalai 1,000 . / Hoto: AA
14 Maris 2024

Hukumar ba da agaji ta Turkiyya ta kai kayan abinci na watan Ramadan ga ma'aikatar Waƙafi da Harkokin Addini ta Falasdinu da za a raba wa iyalai 1,000 da ke zaune a sansanonin 'yan gudun hijira a garuruwa daban-daban na Falasɗinu.

Orhan Aydin, jami'in Hukumar Hadin Kan Turkiyya TIKA a Falasdinu, ya bayyana a ranar Alhamis cewa, za su ci gaba da bai wa al'ummar Falasdinu goyon baya a duk tsawon watan Ramadan.

Ya ce za su gudanar da ayyuka kamar rabon abinci da samar da kayan abinci da shirya buɗa-baki a sassa daban-daban na Falasdinu ciki har da Gaza.

A wani bangare na tallafin na watan Ramadan, hukumar agajin ta kuma ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Al Amari, wanda a baya-bayan nan ke fama da hare-hare, tare da raba kayan abinci ga iyalai mabuƙata.

Matsanancin ƙarancin abinci da ruwa mai tsafta da magunguna

Wahalhalun zamantakewa da tattalin arziki da suka samo asali daga manufofin mamayar da Isra'ila ta daɗe tana yi a Yammacin Gaɓar Kogin Jordan da ta mamaye da kuma yakin Gaza na ci gaba da tsananta.

Isra'ila ta ƙaƙaba wa yankin Falasdinawa wani takunkumin hana fita, lamarin da ya bar al'ummarta, musamman mazauna arewacin Gaza cikin barzanar faɗawa cikin matsananciyar yunwa.

Yaƙin Isra'ila ya jefa kashi 85 cikin 100 na al'ummar Gaza zuwa matsugunin cikin gida a cikin matsanancin ƙarancin abinci da ruwan sha mai tsafta, da kuma magunguna, yayin da aka lalata yawancin ababen more rayuwa a yankin, a cewar MDD.

Baya ga ƙaruwar rashin aikin yi da fatara bayan yaƙin, matsin lamba da hare-haren da ake kai wa garuruwa kamar Jenin da Tulkarm da Qalqilya da Tubas da Nablus da Ramallah, musamman ma sansanonin 'yan gudun hijira a wadannan garuruwa na ƙara ta'azzara.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista
Turkiyya na da rawar da za ta taka a tsaron Turai, ta shirya domin aikin Gaza: Ministan Tsaro
Turkiyya ta yi maraba da amincewar majalisar dokokin TRCN kan ƙudurin samar da ƙasashe biyu
Ya kamata amincewar Ƙasashen Yamma da Falasɗinu ta zama silar samar da mafita ta ƙasa biyu: Erdogan
Jami'an Turkiyya da Syria sun gudanar da tattaunawa kan tsaro a Ankara
Turkiya na goyon bayan duk wani ƙoƙari na kawo ƙarshen kisan kiyashi a Gaza: Erdogan