| hausa
TURKIYYA
4 MINTI KARATU
Kafar watsa labaran Turkiyya ta TRT ta yi taron 'Daren Falasɗinu a Ramadan'
"Ko ba daɗe ko ba jima, Isra'ila za ta fahimci cewa ba za ta ɗore ba a zubar da jinin yara da take yi," in ji Darakta Janar na TRT Mehmet Zahid Sobaci, yayin da yake jawabi a taron "Daren Falasdinu a watan Ramadan" a Istanbul.
Kafar watsa labaran Turkiyya ta TRT ta yi taron 'Daren Falasɗinu a Ramadan'
An nuna wasu shirye-shirye kan rikicin Isra'ila da Falasdinu a yayin taron kamar su "Digital Occupation," "Zionism: Manufacturing A State," "Rafah: An Unsafe Haven," "The Sole Survivor," da kuma "Witness."
22 Maris 2024

Gidan rediyo da talabijin na kasar Turkiyya TRT ya shirya wani taron Ramadan na musamman ga Falasdinu da kuma irin gwagwarmayar da al'ummar Falasdinu ke fuskanta a cikin hare-haren da Isra'ila ke ci gaba da kai musu.

A yayin taron "Daren Falasdinu a watan Ramadan" da aka gudanar a ofishin TRT Ulus da ke Istanbul a ranar Juma'a, babban daraktan TRT Mehmet Zahid Sobaci, ya bayyana irin takaicin da yake ji dangane da yaƙin da Isra'ila ke yi a kan Falasɗinawa.

Ya ce, ko ba daɗe ko ba jima, Isra'ila za ta gane cewa ba za ta ɗore tana zubar da jinin yaran da ba su ji ba ba su gani ba.

Sobaci ya ce "Yayin da muke azumin watan Ramadan, zukatanmu na cikin bakin ciki ga halin da 'yan'uwanmu Falasdinu ke ciki na tsananin wahala."

"A yau, muna goyon bayan wadanda ke Gaza da Rafah, da Yammacin Kogin Jordan, muna jaddada cewa ba su kadai ba ne a gwagwarmayar da suke yi."

Sobaci ya kuma soki labaran son zuciya da kafafen yada labarai na Yammacin Duniya ke yadawa. “Duk da gurbatattun bayanan da kafafen yada labarai na Yamma ke yi, mun tsaya tsayin daka wajen bayyana cikakkiyar gaskiya.

Yunkurin da Isra'ila ke yi na ɓoye ayyukanta ba zai iya ɓoye irin ta'asar da ke faruwa a idon duniya ba. Kisan gillar da suke neman boyewa ya bayyana a fili."

Ya ƙara da cewa, "Wannan halin da ake ciki yana nuna rashin tarbiyya da ɗa'a a tsakanin al'ummomin Yammacin Duniya, wadanda ke da'awar kiyaye dabi'un bil'adama na duniya amma galibi suna kasawa a aikace."

"Mun shaida yadda ake amfani da manufar 'yancin fadin albarkacin baki a wasu lokuta a Yammacin Duniya. 'Yancin fadin gaskiya ya wuce iyakokin al'adu kuma ya kamata a yi nasara a duniya," in ji Sobaci.

'Barnar da Isra'ila ta yi a Gaza ta wuce kashi 70 cikin 100'

Da yake jawabi a wajen taron da TRT ta shirya, jakadan Falasdinu a Turkiyya, Dr. Faed Mustafa, ya nanata taken shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan da ke cewa "Duniya ta fi biyar girma" ya kuma ce, "Tsarin kasa da kasa da ake gudanarwa a halin yanzu bai ceci Falasdinawa ba kuma bai cimma adalci ba. "

Jakadan ya ƙara da cewa "Wannan zaluncin zai kawo ƙarshe ne a lokacin da Falasdinawa za su iya samar da 'yantacciyar kasar Falasdinu tare da Kudus a matsayin babban birninta."

"Muna magana ne game da lalata fiye da kashi 70 cikin 100 na ƙasar Gaza. Barnar ta shafi komai a Gaza, ciki har da asibitoci da jami'o'i da makarantu da masallatai da kuma majami'u.

Ba su bar komai ba a Gaza," in ji Mustafa. "Gaskiya mu Falasdinawa muna fuskantar mawuyacin hali tsawon watanni shida.

Duk da haka, zaluncin nan ba a ranar 7 ga Oktoba ya fara ba.” A yayin taron, an nuna fina-finai guda biyar, masu dauke da taken "Digital Occupation," da "Zionism: Manufacturing A State," da "Rafah: An Un Safe Haven," da "The Sole Survivor," da kuma "Witness."

Bugu da ƙari, an kuma nuna tallar sauran fina-finan da ke tafe. Fina-finan sun ba da haske kan bangarori daban-daban na rikicin Isra'ila da Falasdinu.

MAJIYA:TRT World
Rumbun Labarai
An karrama sojojin Turkiyya da suka yi shahada a hatsarin jirgin sama a iyakar Azerbaijan da Georgia
Sojojin Turkiyya 20 sun yi shahada a hatsarin jirgin soji na dakon kaya a Georgia: Ma’aikatar Tsaro
Jirgin dakon kaya na sojin Turkiyya ya yi hatsari a iyakar Georgia-Azerbaijan dauke da jami'ai 20
Turkiyya na jimamin tunawa da rasuwar Ataturk shekara 87 da suka wuce
Nasarar da aka samu a yankin Karabakh na Azerbaijan babbar nasara ce ga yankin Caucasus: Erdogan
Turkiyya ta yi umarnin kama Firaministan Isra'ila Netanyahu da wasu mutane kan kisan kiyashi a Gaza
Turkish Airlines ya sayi hannun jari na dala miliyan 355 a kamfanin Air Europa na Spain
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan