| hausa
TURKIYYA
4 MINTI KARATU
Yaya aminci da ingancin zaɓuka suke a Turkiyya?
Turkiyya ta shirya gudanar da ƙananan zaɓuka masu muhimmanci waɗanda za a yi a ranar Lahadi mai zuwa, inda za a kammala yaƙin neman zabe a ranar 30 ga Maris, kwana guda kafin zaben.
Yaya aminci da ingancin zaɓuka suke a Turkiyya?
Jam'iyyun siyasa za su aike da gwamman dubunnan masu sanya idanu a cibiyoyin jefa kuri'a. /Hoto: AA Archive
26 Maris 2024

Masu jefa kuri'a a Turkiyya za su zabi magadan gari da magadan garin gundumomi da masu unguwanni a zabukan.

Tare da jam'yyu 35 da suke takara a zabukan, Hukumar Zabe ta Koli ta bayyana cewa kuri'u 350 ne kadai za a jefa a kowanne akwatin zabe a yayin zabukan gama-gari da kanana.

Wannan mataki ya dogara ne kan fahimtar cewa masu jefa kuri'a a akwatin zabe za su iya jefa kuri'a a lokacin nau'in zabuka biyu.

Muna kokarin ganin an gudanar da sahihin zabe na gaskiya a Turkiyya.

Gudanar da zabuka

Hukumar zabe ta YSK ta samar da wani tsari na tabbatar da ingancin kuri'u, farawa daga akwatunan zabe.

A kowanne bakin akwati, akwai mutane biyar da suka hada da wakilan YSK da na manyan jam'yyun siyasa na zaune don sanya idanu. Mutanen na duba katin dan aksa na mutum da tabbatar da akwai sunansa a rejistar zabe.

Wannan na hana mutum ya jefa kuri'a sau biyu. Yana kuma taimaka wa wajen amincewa da sakamako tsakanin wakilan jam'yyu da ke wajen.

Jam'yyun siyasa, ciki har da jam'iyya mai mulki ta AKP da babbar jam'yyar adawa ta CHP, suna tura gwamman dubunnan masu sanya idanu zuwa cibiyoyin jefa kuri'a.

Dubban masu sanya idanu za su bibiyi zabukan

A yayin da zabukan ke ƙaratowa, jam'iyyun sun dauki 'yan sa-kai, musamman don wannan manufa. Wadannan wakilai na da izinin su raka kuri'u zuwa wajen sanar da sakamako.

Baya ga wakilan jam'iyya da na Hukumar Zabe, kungiyoyi masu zaman kansu ma na da nasu 'yan sa-kai da suke sanya idanu kan zaben.

A lokacin da aka fara kirga kuri'u, wakilai 'yan sa-kai na jam'iyyu na zaune a wajen. Za su iya tabbatar da ko kuri'un da aka kirga sun yi daidai da sakamakon da ke hannun su ko akasin haka, za su iya daukar hotuna tare da mika bayanai ga jagororin jam'iyya na sama.

Abin da ya sanya gudanar da zaben zama mara rikici shi ne wanzuwa masu sanya idanu masu cin gashin kansu, ciki har da mutane 40 daga Majalisar Tarayyar Turai, da kuma Kungiyar Hadin Kan Tsaro ta Turai, wadanda suke zuwa bisa gayyatar da gwamnati ta yi musu.

A farkon wannan watan aka sake tabbatar da 'yancin YSK, a lokacin da ta ki amincewa da bukatar gwamnati na sanin wajen da aka ajje kuri'u, a yayin da ake sauraren gudanar da zaben.

'Yan adawa sun nuna rashin amincewa kan lallai kar a sanar da Ma'aikatar Harkokin Cikin Gida a ina kuri'un suke.

Wannan na nuni da cewa ma'aikatar hukumar zabe na gudanar da ayyukansu busa 'yanci ba tare da katsalandan din gwamnati ko jami'anta ba.

Domin kauce wa duk wani nau'i na rikici, kamfanin dillancin labarai na Anadolu mallakin gwamnati ne kadai aka yarda ya saki sakamakon zabe.

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
Nasarar da aka samu a yankin Karabakh na Azerbaijan babbar nasara ce ga yankin Caucasus: Erdogan
Turkiyya ta yi umarnin kama Firaministan Isra'ila Netanyahu da wasu mutane kan kisan kiyashi a Gaza
Turkish Airlines ya sayi hannun jari na dala miliyan 355 a kamfanin Air Europa na Spain
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista
Turkiyya na da rawar da za ta taka a tsaron Turai, ta shirya domin aikin Gaza: Ministan Tsaro