| hausa
AFIRKA
3 MINTI KARATU
An kama wasu ƴan Nijeriya 'kan kai wa ƴan sandan Afirka ta Kudu farmaki'
'Yan sanda a Afirka ta Kudu sun ce waɗanda aka kama ɗin sun yi ƙoƙarin ɗaukar fansa ne, bayan da 'yan sandan suka kama wani ɗan Nijeriya kan zargin mu'amala da miyagun ƙwayoyi.
An kama wasu ƴan Nijeriya 'kan kai wa ƴan sandan Afirka ta Kudu farmaki'
An lalata motocin 'yan sandan Afirka ta Kudu a harin. / Hoto: Getty Images
19 Afrilu 2024

'Yan sanda a Afirka ta Kudu sun ce sun kama 'yan Nijeriya su takwas bisa zargin ta da fitina da ɓarnata kadarori, bayan da suka far ma 'yan sanda.

Waɗanda ake zargin sun lalata motocin 'yan sanda kuma suka fasa tagogin ofishin 'yan sanda na Kimberley a daren Alhamis.

'Yan sandan sun ce waɗanda aka kama ɗin sun kawo harin ɗaukar fansa ne bayan da jami'ansu suka kama wani ɗan Nijeriya kan zargin mu'amala da miyagun ƙwayoyi.

Kakakin Gundumar SAPS, Cherelle Ehlers ta ce, "Lokacin aiwatar da kamen, wanda aka zo kamawa ya yi yunƙurin bijirewa, kuma ya doki jami'an SAPS ɗin da bulalar taya. Wasu gungun mutane da ake kyautata zaton 'yan Nijeriya ne sun far wa jami'an suka lalata motocinsu."

Jami'ar ta ƙara da cewa, "'Yan sanda sun harba harsashin roba don tarwatsa mutanen... a yayin hakan, mutanen sun fasa tagogin caji ofis ɗin. Gungun mutanen sun tunkaro ofishin kuma suka yi barazanar ɗaukar fansa.

"Kwamandan samamen ya gargaɗi mutanen da su watse. Sannan bayan tafiyarsu, mutanen sun lalata motocin 'yan sanda... kuma an kama ƙarin mutane huɗu bisa zargin ɓarnata kadarori."

Kwamishinan 'Yan Sanda na Gundumar Northern Cape, Laftanal Janar Otola ya yi Allah-wadai da wannan ɗabi'a, kuma ya jaddada cewa duk wanda ya hana 'yan sanda aiwatar da ayyukansu za a hukunta shi bisa doka.

Otola ya ƙara da cewa, "Ba za mu bar irin wannan ɗabi'a ta yi wa doka karan-tsaye ba; muna aiki tare da Ma'aikatar Cikin gida don tantance ko waɗanda ake zargin suna da halaccin zama a ƙasar nan.

"Ƴan sanda za su ci gaba da ɗabbaƙa ƙarfin hukumar ƙasa a Gundumar Northern Cape."

MAJIYA:TRT Afrika
Rumbun Labarai
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi
WHO ta bayyana damuwa kan karuwar masu ciwon siga a Afirka
Kisan kare dangi a boye da bayyane: Gushewar jinkai a Al Fasher
An ba da belin dan Gaddafi bayan da ya shafe shekaru 10 a tsare a Lebanon
Gwamnatin Trump 'ta aika wa Equatorial Guinea dala miliyan 7.5' don ta karɓi waɗanda Amurka ta kora
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta