AFIRKA
3 MINTI KARATU
An ƙara wa sojojin Burkina Faso wa'adin shekaru biyar a kan mulki
Sojojin Burkina Faso sun ƙwace mulki a shekarar 2022 sannan suka yi alƙawarin gudanar da zaɓe a watan Yulin wannan shekarar domin komawa turbar dimokuraɗiyya, sai dai sun ce shawo kan rashin tsaron ƙasar shi ne babban abin da suka sanya a gaba.
An ƙara wa sojojin Burkina Faso wa'adin shekaru biyar a kan mulki
Sabuwar dokar ta amince Ibrahim Traore ya tsaya takara a zaɓen da za a gudanar. /Hoto:Reuters

Gwamnatin mulkin soji ta Burkina Faso za ta ci gaba da mulki nan da shekaru biyar masu zuwa bayan mahalarta taro kan makomar ƙasar da aka yi ranar Asabar sun bayar da shawarar komawa kan mulkin dimokuraɗiyya zuwa watanni 60 daga watan Yuli mai kamawa.

Wannan shawara na cikin wata takarda da mahalarta taron suka amince da ita, wadda za ta kasance wani sabon tsari na gudanar da mulki a ƙasar.

Sojojin Burkina Faso sun ƙwace mulki a shekarar 2022 sannan suka yi alƙawarin gudanar da zaɓe a watan Yulin wannan shekarar domin komawa turbar dimokuraɗiyya, sai dai sun ce shawo kan rashin tsaron ƙasar shi ne babban abin da suka sanya a gaba.

Sabon tsarin, wanda shugaban mulkin sojin Burkina Faso Ibrahim Traore ya sanya wa hannu, ya nuna cewa za a mayar da mulki hannun gwamnatin farar-hula cikin watanni 60 daga ranar 2 ga watan Yuli.

"Za a gudanar da zaɓuka kafin wannan lokaci idan lamuran tsaro suka inganta," a cewar sabuwar dokar.

Sabuwar dokar ta amince Ibrahim Traore ya tsaya takara a zaɓen da za a gudanar.

Jinkirta lokacin gudanar da zaɓen yana iya sanya fargaba a zukatan masu rajin mulkin dimokuraɗiyya a Yammaci da Tsakiyar Afirka, inda aka gudanar da juyin mulki sau takwas a cikin shekaru huɗu da suka gabata.

Rashin tsaro na ci gaba da ƙarami a yankin Sahel na Yammacin Afirka irin su Burkina Faso, Mali da Nijar da ke makwabtaka da juna sakamakon hare-haren ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar-baya da ke da alaƙa da al Qaeda da Islamic State.

Burkina Faso ta yi fama da ƙaruwar hare-hare na ƙungiyoyin ta'adda a 2023, inda suka kashe sama da mutum 8,000, a cewar ƙungiyar ACLED da ke bin diddigin hare-haren 'yan ta'adda, mai mazauni a Amurka.

MAJIYA:AFP
Rumbun Labarai
Ƙasashe fiye da 20 sun yi Allah wadai da RSF kan kashe-kashen da take yi a Sudan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi kira da a dakatar da zubar da jini a Sudan
Paul Biya na Kamaru: Dan siyasar da zai ci gaba da yin mulki har sai ya kai shekara 99?
Hare-haren RSF sun kori ƙarin dubban mutane daga Darfur da Kordofan na Sudan
RSF ta binne gawawwaki a kabarin bai-ɗaya, ta ƙone wasu domin 'ɓoye laifukan yaƙi': Likitocin Sudan
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista