Saulos Chilima: Gwamnatin Malawi ta ayyana  kwanaki 21 na makokin mataimakin shugaban ƙasar

Tun daga ranar Talata 11 ga watan Yuni ne aka soma makokin zuwa ranar Litinin 1 ga watan Yuli, a cewar sanarwar da majalisar ministocin Malawi ta fitar a ranar Talata.

By Shamsiyya Ibrahim
‘Yan uwan wadanda suka mutu a hatsarin jirgin saman sun hallara  a babban filin tashi da saukar jiragen sama na babban birnin kasar, Lilongwe, domin tarban gawarwakin a yammacin ranar Talata. Hoto / Gwamnatin Malawi        / Others

Gwamnatin Malawi ta ayyana kwanaki 21 na makoki a fadin ƙasar don girmama mataimakin shugaban ƙasar Saulos Chilima da wasu mutane takwas da suka mutu a hatsarin jirgin sama.

Da safiyar ranar Litinin ne jirgin sojin da ya ɗauko mataimakin shugaban ƙasar da tawagarsa ya yi ɓatan-dabo, bayan da ya gaza sauka saboda rashin kyawun yanayi.

Jirgin ya tashi ne daga babban birnin ƙasar Lilongwe zuwa Mzuzu wanda ke da tazarar kilomita 230, inda za a yi jana’izar wani tsohon ministan ƙasar.

An tsinci sauran tarkacen jirgin ne a ranar Talata a cikin wani babban daji mai tsaunuka da ke kusa da garin Mzuzu.

An soma makoki na ƙasa baƙi ɗaya ne daga ranar Talata 11 ga watan Yuni zuwa ranar Litinin 1 ga watan Yuli, kamar yadda majalisar ministocin ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata.

Yin ƙasa da tutar ƙasar

Shugaban ƙasar Lazarus Chakwera ya ba da umarni a yi ƙasa-ƙasa da tutar ƙasar a ko ina a fadin ƙasar har tsawon lokacin makokin.

Majalisar ministocin ƙasar ta ce daga baya za a fitar da cikakken bayani game da lokacin da za a yi jana'izar waɗanda suka mutu a hatsarin.

An kai gawar Chilima da 'yan tawagarsa da suka mutu zuwa babban birnin ƙasar Lilongwe.

Shugaba Chakwera ya samu rakiyar ministocin gwamnati da wasu jami'ai domin karɓar gawawwakin a filin jirgin saman Kamuzu a yammacin ranar Talata.

Manyan shugabannin duniya sun yi ta miƙa saƙon ta'aziyyarsu ga iyalai da kuma gwamnatin ƙasar ta Malawi.